BindiddigiShin Nijar ta rabu da Faransanci?

Shin Nijar ta rabu da Faransanci?

-

Tun bayan labarin amincewa da kuma ayyana Hausa a matsayin harshen kasa mutane ke ta wallafa labarin cewa Nijar ta bar harshen Faransanci.
To sai dai  ba kamar yadda wasu suka fahimci labarin ba ga yadda abin yake.
A yanzu dai kasar ta Nijar ta tabbatar da cewa Hausa ta zama harshen ƙasa wato langue nationale a Faransanci.

Wannan na nufin cewa harshen Hausa an amince shi a matsayin harshen da ke da muhimmanci wajen adana al’adu, sadarwa a tsakanin jama’a, da koyar da ilimi a matakin farko wato firamare amma hakan ba yana nufin baza’a koyar da yaren Faransanci ba. Haka zalika kasar ta bayyana wasu yaruka a kasar a matsayin masu muhimmanci.

Amfani da Hausa a matsayin harshen ƙasa yana nufin za a iya amfani da shi a:

Makarantun firamare.

Za’a dinga sadarwa da shirye-shirye a rediyo da Talabijin.

Tattaunawa tsakanin al’umma da hukumomi a matakin ƙasa.

Wayar da kan mutane kan wasu al’amuran da suka shafe su ko suka shafi kasa.

To amma inda gizo ke sakar shine harshen Faransanci har yanzu shine harshen aiki wato langues de travail a Faransanci.

Faransanci shine harshen da gwamnati za ta cigaba da amfani da shi wajen:
To amma fa baya ga Faransanci kasar ta kara da Turancin Ingilishi a matsayin harshen gwamnati.

sune dai za’a dinga;

Rubuce-rubuce a hukumance.

Takardun gwamnati da dokoki.

Tattaunawa da kasashen waje.

Zaman kotu da yanke hukunci a kotu.

Rubutu da karatu a jami’o’i da sauran manyan makarantu.

Kasar ta Nijar dai ba ta cire Faransanci a matsayin yaren gwamnati ba sai dai kara harshen turancin Ingilishi kamar yadda kasar Algeria tayi inda ake koyar da yara yarukan biyu a makarantu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya da suka shafi bangarorin biyu wato bangaren Sarki Aminu Ado...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan kiyashin kiristoci a Najeriya da kuma bayanin yiwuwar turo da...

Bidiyon Nnamdi Kanu a gidan yarin Sokoto haɗin AI ne 

Bayan hukuncin da koto tayi na ɗaure Nnamdi Kanu bisa laifin ta'addanci, hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta...

Rasha da Amurka ne kan gaba wajen yaɗa labaran ƙarya a yammacin Afirka cewar Fauziyya Kabir Tukur

Shekara da shekaru ƙasashen duniya kanyi amfani da yaɗa labarai wajen yaƙi da juna ko haddasa rikici a wasu...

ƙirƙirarrayir basirar AI wanne hali Najeriya ke ciki?

A cikin watan Satumba, 2025 aka samu wani shafi na caca ya ƙirƙiri bidiyo da hoton talla na ƙarya...

Ƙarya ne: Saudiyya bata cire ɗarikar Tijjaniyya daga cikin akidu da ke da alaka da musulunci ba

Wani shafin TikTok mai suna prince hassan ya wallafa labarin cewa hukumar Saudiyya ta cire Tijjaniyya cikin jerin akidun...

Karanta wannan

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar