BindiddigiShin Nijar ta rabu da Faransanci?

Shin Nijar ta rabu da Faransanci?

-

Tun bayan labarin amincewa da kuma ayyana Hausa a matsayin harshen kasa mutane ke ta wallafa labarin cewa Nijar ta bar harshen Faransanci.
To sai dai  ba kamar yadda wasu suka fahimci labarin ba ga yadda abin yake.
A yanzu dai kasar ta Nijar ta tabbatar da cewa Hausa ta zama harshen ƙasa wato langue nationale a Faransanci.

Wannan na nufin cewa harshen Hausa an amince shi a matsayin harshen da ke da muhimmanci wajen adana al’adu, sadarwa a tsakanin jama’a, da koyar da ilimi a matakin farko wato firamare amma hakan ba yana nufin baza’a koyar da yaren Faransanci ba. Haka zalika kasar ta bayyana wasu yaruka a kasar a matsayin masu muhimmanci.

Amfani da Hausa a matsayin harshen ƙasa yana nufin za a iya amfani da shi a:

Makarantun firamare.

Za’a dinga sadarwa da shirye-shirye a rediyo da Talabijin.

Tattaunawa tsakanin al’umma da hukumomi a matakin ƙasa.

Wayar da kan mutane kan wasu al’amuran da suka shafe su ko suka shafi kasa.

To amma inda gizo ke sakar shine harshen Faransanci har yanzu shine harshen aiki wato langues de travail a Faransanci.

Faransanci shine harshen da gwamnati za ta cigaba da amfani da shi wajen:
To amma fa baya ga Faransanci kasar ta kara da Turancin Ingilishi a matsayin harshen gwamnati.

sune dai za’a dinga;

Rubuce-rubuce a hukumance.

Takardun gwamnati da dokoki.

Tattaunawa da kasashen waje.

Zaman kotu da yanke hukunci a kotu.

Rubutu da karatu a jami’o’i da sauran manyan makarantu.

Kasar ta Nijar dai ba ta cire Faransanci a matsayin yaren gwamnati ba sai dai kara harshen turancin Ingilishi kamar yadda kasar Algeria tayi inda ake koyar da yara yarukan biyu a makarantu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labaran ƙarya ne ke haddasa ƙiyayya tsakanin ‘yan kudu da ‘yan arewa

Shekara da shekaru dai ana samun rasa rayuka da dukiyoyin al’ummar arewacin Najeriya a kudancin kasar. Abubuwan da suka...

Labaran karya daga Burkina Faso na cigaba da yaduwa a Najeriya

  Da dama daga ‘yan Najeriya masu amfani da kafafen sada zumunta na cin karo da labarai kala-kala dangane da...

Najeriya-Saudiyya sun karyata labarin cewa za’a hana ‘yan kasar bizar shiga Saudiyya

Ma’aikatar harkokin wajen Najeriya ta karyata ikirarin karya da ke yawo a kafafen sadarwa na zamani, wanda ke cewa...

Ina gaskiyar cewa Amurka, Faransa ke neman haddasa faɗa tsakanin Sudan da Chadi?

  Duk lokacin da aka sami wata hatsaniya ko rikici tsakanin kasashe, wasu na amfani da wannan dama wajen yada...

Bidiyon ƴan sanda sunyi kame a Edo ƙarya ne, bidiyon ya faru a Ghana ne

  A yayin da ƴan Najeriya ke cigaba da Allah wadai da kisan wasu matafiya a jihar Edo, wasu na...

Waɗanne ƙasashe ne ke rura wutar yaƙin Sudan?

Yaƙin Sudan dai ana yin sane tsakanin dakarun sojin ƙasar wanda  Janar Abdul Fatah Al-Burhan ke shugabanta kuma shine...

Karanta wannan

Labaran ƙarya ne ke haddasa ƙiyayya tsakanin ‘yan kudu da ‘yan arewa

Shekara da shekaru dai ana samun rasa rayuka da...

Labaran karya daga Burkina Faso na cigaba da yaduwa a Najeriya

  Da dama daga ‘yan Najeriya masu amfani da kafafen...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar