BindiddigiShin Najeriya ce ta uku cikin ƙasashen da aka...

Shin Najeriya ce ta uku cikin ƙasashen da aka fi kai hare-haren ta’addanaci a duniya?

-

Hukunci: Ƙarya ne
Wannan yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa ikirari cewa Najeriya ce ta uku cikin ƙasashen da aka fi kai hare-haren ta'addanaci a duniya ƙarya ne.
Najeriya dai na cikin ƙasashen duniya dake fama da matsalar tsaro da hare-haren ta’addanci wanda wasu lokuta kan haddasa labaran ƙarya kan matsalar musamman abinda ya shafi alƙaluma.

Iƙirari:

Akwai dai wani rahoto da gidan jarida na BBC Hausa ya wallafa a shafinsa na Facebook a ranar 7/03/2025 inda cikin rahoton yace Najeriya ce ta uku cikin ƙasashen da aka fi kai hare-haren ta’addanaci a duniya sai kuma ƙasar Nijar ta biyar.
Wallafar dai ta sami tofa albarkacin baki wato comment dubu daya da dari biyar da kuma shares sama da dari da casa’in.
Labarin dake yaduwa.
Labarin dake yaduwa.
Bincike:
Kafar tantance labarai, bindiddigi da bincike ta Alkalanci ta duba rahoton ayyukan ta’addanci na duniya wato Global Terrorism index wanda aka wallafa a ranar 5/03/2025.
A cikin rahoton dai Alkalanci ta gano cewa Najeriya ce ƙasa ta biyar cikin ƙasashen da aka fi kai hare-haren ta’addanaci a duniya maimakon ta uku da BBC tayi ikirari  wacce take biwa ƙasar Nijar wacce take a matsayi na biyar.
Rahoton GTI dake nuna Najeriya ce ta shida,
Rahoton GTI dake nuna Najeriya ce ta shida,
Rahoton dai ya ce an sami raguwar hare-haren ta’addanci da kashi 37 to amma kashe-kashe ya karu da kashi 6 wanda rahoton yace mutanen da suka mutu sanadiyyar ta’addanci sun kai 565 a shekarar 2024. Wanda shine mafi yawa tun shekarar 2020.
Rahoton ya alakanta hakan da rikici tsakanin mayakan Boko Haram da ISWA, domin kuwa kashe-kashe dake da alaka da kungiyoyin biyu shine kaso mafi girma wato kashi 60.
Rahoton GTI kan ta’addanci a Najeriya.
Rahoton GTI kan ta’addanci a Najeriya.

Yaushe aka wallafa rahoton? 

Sannan a rahoton na BBC sun bayyana cewa an wallafa rahoton a 5 ga watan Mayu duk da cewa ba’a rubuta watan Mayun wacce shekara ba. To sai dai Alkalanci ta gano cewa rahoton dai an wallafa shi ne a 5 ga watan Maris din shekarar 2025.

Sakamakon bincike:

Bisa alkaluman da rahoton na GTI ya fitar, a gaba daya cikin rahoton babu inda aka bayyana Najeriya a matsayi kasa ta uku cikin jerin ƙasashen da aka fi kai hare-haren ta’addanaci a duniya. Rahoton ya sanya ta a matsayi na shida wato tana biwa Nijar dake matsayi na biyar.
Wannan yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa ikirari cewa Najeriya ce ta uku cikin ƙasashen da aka fi kai hare-haren ta’addanaci a duniya ƙarya ne.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Ina gaskiyar labari da hotunan baiwa ƴan wasan Super Eagles gidaje da motoci

Bayan da aka kammala gasar cin kofin Nahiyar Afirka AFCON wanda Najeriya ta zo ta biyu, akwai labarai kala-kala...

Bidiyon da ake yaɗawa ba na waɗanda sukai kisan Ɗorayi bane 

Ƴan Najeriya dai na cigaba da jimami tare da Allah wadai da kisan wasu ƴan gida ɗaya su bakwai...

Hotunan samuwar makaman kariya zuwa Burkina Faso daga Rasha da China hadin AI ne

  Yayin da Rasha da ƙasar Sin ke ci gaba da tura makamai zuwa yankin Sahel, wani hoto da bidiyo...

Labarin cewa Aisha Buhari ta amince ta auri Sheikh Isa Ali Pantami ƙarya ne

Tun bayan kammala iddar tsohuwar matar shugaban kasa Muhammadu Buhari ake ta yada wasu labarai da iƙirarai kala-kala wanda...

Gwamna Abba Kabir Yusuf bai cire Mustapha Kwankwaso daga muƙaminsa ba

A ƙarshen watan Disemba ne dadi aka sami labarin cewa gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf zai sauya sheƙa...

Me yasa Amurka ta kai hari Sokoto?

Kasar Amurka ta takaddamar da hare-hare a wasu yankuna a arewacin Najeriya. Yanku nan sun hada da Arewa maso...

Karanta wannan

Ina gaskiyar labari da hotunan baiwa ƴan wasan Super Eagles gidaje da motoci

Bayan da aka kammala gasar cin kofin Nahiyar Afirka...

Bidiyon da ake yaɗawa ba na waɗanda sukai kisan Ɗorayi bane 

Ƴan Najeriya dai na cigaba da jimami tare da...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar