BindiddigiShin Najeriya ce ta uku cikin ƙasashen da aka...

Shin Najeriya ce ta uku cikin ƙasashen da aka fi kai hare-haren ta’addanaci a duniya?

-

Hukunci: Ƙarya ne
Wannan yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa ikirari cewa Najeriya ce ta uku cikin ƙasashen da aka fi kai hare-haren ta'addanaci a duniya ƙarya ne.
Najeriya dai na cikin ƙasashen duniya dake fama da matsalar tsaro da hare-haren ta’addanci wanda wasu lokuta kan haddasa labaran ƙarya kan matsalar musamman abinda ya shafi alƙaluma.

Iƙirari:

Akwai dai wani rahoto da gidan jarida na BBC Hausa ya wallafa a shafinsa na Facebook a ranar 7/03/2025 inda cikin rahoton yace Najeriya ce ta uku cikin ƙasashen da aka fi kai hare-haren ta’addanaci a duniya sai kuma ƙasar Nijar ta biyar.
Wallafar dai ta sami tofa albarkacin baki wato comment dubu daya da dari biyar da kuma shares sama da dari da casa’in.
Labarin dake yaduwa.
Labarin dake yaduwa.
Bincike:
Kafar tantance labarai, bindiddigi da bincike ta Alkalanci ta duba rahoton ayyukan ta’addanci na duniya wato Global Terrorism index wanda aka wallafa a ranar 5/03/2025.
A cikin rahoton dai Alkalanci ta gano cewa Najeriya ce ƙasa ta biyar cikin ƙasashen da aka fi kai hare-haren ta’addanaci a duniya maimakon ta uku da BBC tayi ikirari  wacce take biwa ƙasar Nijar wacce take a matsayi na biyar.
Rahoton GTI dake nuna Najeriya ce ta shida,
Rahoton GTI dake nuna Najeriya ce ta shida,
Rahoton dai ya ce an sami raguwar hare-haren ta’addanci da kashi 37 to amma kashe-kashe ya karu da kashi 6 wanda rahoton yace mutanen da suka mutu sanadiyyar ta’addanci sun kai 565 a shekarar 2024. Wanda shine mafi yawa tun shekarar 2020.
Rahoton ya alakanta hakan da rikici tsakanin mayakan Boko Haram da ISWA, domin kuwa kashe-kashe dake da alaka da kungiyoyin biyu shine kaso mafi girma wato kashi 60.
Rahoton GTI kan ta’addanci a Najeriya.
Rahoton GTI kan ta’addanci a Najeriya.

Yaushe aka wallafa rahoton? 

Sannan a rahoton na BBC sun bayyana cewa an wallafa rahoton a 5 ga watan Mayu duk da cewa ba’a rubuta watan Mayun wacce shekara ba. To sai dai Alkalanci ta gano cewa rahoton dai an wallafa shi ne a 5 ga watan Maris din shekarar 2025.

Sakamakon bincike:

Bisa alkaluman da rahoton na GTI ya fitar, a gaba daya cikin rahoton babu inda aka bayyana Najeriya a matsayi kasa ta uku cikin jerin ƙasashen da aka fi kai hare-haren ta’addanaci a duniya. Rahoton ya sanya ta a matsayi na shida wato tana biwa Nijar dake matsayi na biyar.
Wannan yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa ikirari cewa Najeriya ce ta uku cikin ƙasashen da aka fi kai hare-haren ta’addanaci a duniya ƙarya ne.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Shin Nijar ta rabu da Faransanci?

Tun bayan labarin amincewa da kuma ayyana Hausa a matsayin harshen kasa mutane ke ta wallafa labarin cewa Nijar...

Labaran ƙarya ne ke haddasa ƙiyayya tsakanin ‘yan kudu da ‘yan arewa

Shekara da shekaru dai ana samun rasa rayuka da dukiyoyin al’ummar arewacin Najeriya a kudancin kasar. Abubuwan da suka...

Labaran karya daga Burkina Faso na cigaba da yaduwa a Najeriya

  Da dama daga ‘yan Najeriya masu amfani da kafafen sada zumunta na cin karo da labarai kala-kala dangane da...

Najeriya-Saudiyya sun karyata labarin cewa za’a hana ‘yan kasar bizar shiga Saudiyya

Ma’aikatar harkokin wajen Najeriya ta karyata ikirarin karya da ke yawo a kafafen sadarwa na zamani, wanda ke cewa...

Ina gaskiyar cewa Amurka, Faransa ke neman haddasa faɗa tsakanin Sudan da Chadi?

  Duk lokacin da aka sami wata hatsaniya ko rikici tsakanin kasashe, wasu na amfani da wannan dama wajen yada...

Bidiyon ƴan sanda sunyi kame a Edo ƙarya ne, bidiyon ya faru a Ghana ne

  A yayin da ƴan Najeriya ke cigaba da Allah wadai da kisan wasu matafiya a jihar Edo, wasu na...

Karanta wannan

Shin Nijar ta rabu da Faransanci?

Tun bayan labarin amincewa da kuma ayyana Hausa a...

Labaran ƙarya ne ke haddasa ƙiyayya tsakanin ‘yan kudu da ‘yan arewa

Shekara da shekaru dai ana samun rasa rayuka da...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar