BindiddigiShin Jami’an kare haddura ta kasa zasu iya aiki...

Shin Jami’an kare haddura ta kasa zasu iya aiki a hanyoyi mallakar jiha?

-

Akwai dai tataburza a wasu jihohin Najeriya inda wasu ke ganin cewa jami’an hukumar kiyaye haddura ta kasa wato road safety ba zasu iya aiki a kan hanyoyi mallakar jiha ba, duk da cewa ana ganin su a cikin gari suna tsare masu abun hawa tare da cin tararsu.

Kafar tantance labarai ta Alkalanci ta duba wannan lamari inda ta fara da samun sakamakon wata shari’a da kotun daukaka kara dake Asaba jihar Delta tayi a shekarar 2023 wanda tace jami’an na road safety basu da hurumin yin aiki ko kama musu abun hawa a hanyoyi dake mallakar jihohi.
Kotun tayi watsi da daukaka karar hukumar ta FRSC kan shari’a tsakanin hukumar ta FRSC da wani mai suna Darlington Ehikim, shari’a mai lamba CA/AS/276/2019 wacce a baya kotun tarayya dake Owerri ta ce hukumar bata da hurumin aiki a hanyoyin jihohi.
Kotun ta ce jami’an na iya aiki ne kawai a hanyoyi mallakar gwamnatin tarayya.
Hukuncin kotun ya nuna cewa duk jami’an road safety da sukai aiki a hanyoyi mallakar jiha haramtaccen aiki ne kawai sukeyi.
Kotun daukaka kara a Abuja
To amma a wata shari’a da kotun daukaka kara dake Abuja  tayi a shekarar 2024 tace jami’an hukumar na FRSC na iya aiki a dukkan hanyoyin Abuja Kasancewar hanyoyin Abuja suma mallakar gwamnatin tarayya ne.
Kotun tarayya a Bauchi 
Haka zalika a wannan shekarar ta 2025 wata kotun tarayya dake Bauchi ta fitar da wata shari’a dake cewa jami’an FRSC na iya aiki a kowacce irin hanya ta tarayya ko ta jiha amma kotun ta ce a jihar Bauchi.
Wacce ta jagoranci shari’ar mai shari’a Aisha Ibrahim tace masu kara Dr. Ibrahim Danjuma da wani basu bayar da cikakken shaidar cewa hanyar da suke korafin ta gwamnatin jiha ce.
Masana Doka
Lauyoyi a Najeriya dai sun sha jadda cewa jami’an FRSC basu da hurumin aikin a hanyoyi mallakar jihohi wanda suka alakanta rashin sanin ilimin doka da kuma ‘yanci ke sa har jami’an na FRSac ke aiki ba tare da wani turjiya ba.
Yanzu haka ma dai wani lauya a jihar Kano mai suna Abba Hikima ya kai karar hukumar ta FRSC kan aiki a hanyoyi mallakar jiha.
Jami’an FRSC
To sai dai jami’an na FRSC na ganin killace su yin aiki a hanyoyin gwamnatin tarayya bazai haifar da da mai ido ba domin Idan anyi hatsari a hanyoyin jihohi suna kai mutane asibiti.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya da suka shafi bangarorin biyu wato bangaren Sarki Aminu Ado...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan kiyashin kiristoci a Najeriya da kuma bayanin yiwuwar turo da...

Bidiyon Nnamdi Kanu a gidan yarin Sokoto haɗin AI ne 

Bayan hukuncin da koto tayi na ɗaure Nnamdi Kanu bisa laifin ta'addanci, hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta...

Rasha da Amurka ne kan gaba wajen yaɗa labaran ƙarya a yammacin Afirka cewar Fauziyya Kabir Tukur

Shekara da shekaru ƙasashen duniya kanyi amfani da yaɗa labarai wajen yaƙi da juna ko haddasa rikici a wasu...

ƙirƙirarrayir basirar AI wanne hali Najeriya ke ciki?

A cikin watan Satumba, 2025 aka samu wani shafi na caca ya ƙirƙiri bidiyo da hoton talla na ƙarya...

Ƙarya ne: Saudiyya bata cire ɗarikar Tijjaniyya daga cikin akidu da ke da alaka da musulunci ba

Wani shafin TikTok mai suna prince hassan ya wallafa labarin cewa hukumar Saudiyya ta cire Tijjaniyya cikin jerin akidun...

Karanta wannan

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar