BindiddigiKasashe KetareShin Jagora A Jam’iyyar NPP Ta Ghana Aziz Yace...

Shin Jagora A Jam’iyyar NPP Ta Ghana Aziz Yace Duk Limami Ko Sarkin Da Bai Zabi Bawumia Ba Zai shiga Wuta?

-

A yayin da ake shirin zaben shugaban kasa a kasar Ghana ana cigaba da samun karuwar yaduwar ikirari da  labarun karya domin bata wani dan takara Ko jamiyya ko kuma kambama jamiyya ko dan takara.

Batu:

Akwai wani ikirari dake yaduwa a kasar Ghana musamman a yankunan Hausawan kasar inda ake zargin jagora a  jamiyyar NPP dake kula da yankunan Zango wanda mafi akasarin su musulmai da Hausawa ne Aziz Futa da cewa: “Duk Limami ko Sarkin Zango da bai zabi dan takarar shugaban kasa na jamiyyar NPP Dakta Bawumia ba wuta zai shiga.”
Wannan ikirari dai an sanyashi a matsayin hoto tare da sanya tambarin gidan talabijin na Ghana “GHONETV”.

Bincike:

Da farko dai kafar bindiddigi ta Alkalanci mun tuntuni dan jarida a kasar Ghana Idris Abdallah inda ya tuntubi gidan Talabijin na Ghana TV. Gidan Talabijin din dai sun karyata tare da bayyana cewa wannan ikirari da hoto da aka sanya sunansu ba daga gare su bane.
Haka zalika sun kara da cewa tuni sun gayyaci Aziz Futa wanda ya nesanta kansa da wadancan bayanai.
Ni ba malami bane balle na bada wannan fatawa, ni kuma ba Allah bane- balle nasan wadanda zasu shiga wuta Ko Aljannah, ban taba wannan magana ba Sam-Sam, an shafa min ne. Maganar dana fadi shine in yau chief imam ya zama flag bearer na NPP mun sami yan Zango musulman da zasu ce ba musulmin kirki bane, yana bautar turu, bai sallah bai kaza just because ya zama NPP wanga magana na fada kuma nayi repeating.”

Sakamakon Bincike:

Kafar bindiddigi ta Alkalanci bayan bincike inda aka kasa samo faifan sauti inda ya fadi wadancan kalamai, kuma gidan Talabijin na Ghana suka karyata cewa ba daga gurinsu bane haka sannan shi kansa Aziz Futa ya fadi kalaman daya fada, ta yanke hukuncin cewa wannan ikirari karya ne wato Aziz Futa baiyi wadancan kalamai shiga wuta ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Ina gaskiyar labari da hotunan baiwa ƴan wasan Super Eagles gidaje da motoci

Bayan da aka kammala gasar cin kofin Nahiyar Afirka AFCON wanda Najeriya ta zo ta biyu, akwai labarai kala-kala...

Bidiyon da ake yaɗawa ba na waɗanda sukai kisan Ɗorayi bane 

Ƴan Najeriya dai na cigaba da jimami tare da Allah wadai da kisan wasu ƴan gida ɗaya su bakwai...

Hotunan samuwar makaman kariya zuwa Burkina Faso daga Rasha da China hadin AI ne

  Yayin da Rasha da ƙasar Sin ke ci gaba da tura makamai zuwa yankin Sahel, wani hoto da bidiyo...

Labarin cewa Aisha Buhari ta amince ta auri Sheikh Isa Ali Pantami ƙarya ne

Tun bayan kammala iddar tsohuwar matar shugaban kasa Muhammadu Buhari ake ta yada wasu labarai da iƙirarai kala-kala wanda...

Gwamna Abba Kabir Yusuf bai cire Mustapha Kwankwaso daga muƙaminsa ba

A ƙarshen watan Disemba ne dadi aka sami labarin cewa gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf zai sauya sheƙa...

Me yasa Amurka ta kai hari Sokoto?

Kasar Amurka ta takaddamar da hare-hare a wasu yankuna a arewacin Najeriya. Yanku nan sun hada da Arewa maso...

Karanta wannan

Ina gaskiyar labari da hotunan baiwa ƴan wasan Super Eagles gidaje da motoci

Bayan da aka kammala gasar cin kofin Nahiyar Afirka...

Bidiyon da ake yaɗawa ba na waɗanda sukai kisan Ɗorayi bane 

Ƴan Najeriya dai na cigaba da jimami tare da...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar