BindiddigiKasashe KetareShin Jagora A Jam’iyyar NPP Ta Ghana Aziz Yace...

Shin Jagora A Jam’iyyar NPP Ta Ghana Aziz Yace Duk Limami Ko Sarkin Da Bai Zabi Bawumia Ba Zai shiga Wuta?

-

A yayin da ake shirin zaben shugaban kasa a kasar Ghana ana cigaba da samun karuwar yaduwar ikirari da  labarun karya domin bata wani dan takara Ko jamiyya ko kuma kambama jamiyya ko dan takara.

Batu:

Akwai wani ikirari dake yaduwa a kasar Ghana musamman a yankunan Hausawan kasar inda ake zargin jagora a  jamiyyar NPP dake kula da yankunan Zango wanda mafi akasarin su musulmai da Hausawa ne Aziz Futa da cewa: “Duk Limami ko Sarkin Zango da bai zabi dan takarar shugaban kasa na jamiyyar NPP Dakta Bawumia ba wuta zai shiga.”
Wannan ikirari dai an sanyashi a matsayin hoto tare da sanya tambarin gidan talabijin na Ghana “GHONETV”.

Bincike:

Da farko dai kafar bindiddigi ta Alkalanci mun tuntuni dan jarida a kasar Ghana Idris Abdallah inda ya tuntubi gidan Talabijin na Ghana TV. Gidan Talabijin din dai sun karyata tare da bayyana cewa wannan ikirari da hoto da aka sanya sunansu ba daga gare su bane.
Haka zalika sun kara da cewa tuni sun gayyaci Aziz Futa wanda ya nesanta kansa da wadancan bayanai.
Ni ba malami bane balle na bada wannan fatawa, ni kuma ba Allah bane- balle nasan wadanda zasu shiga wuta Ko Aljannah, ban taba wannan magana ba Sam-Sam, an shafa min ne. Maganar dana fadi shine in yau chief imam ya zama flag bearer na NPP mun sami yan Zango musulman da zasu ce ba musulmin kirki bane, yana bautar turu, bai sallah bai kaza just because ya zama NPP wanga magana na fada kuma nayi repeating.”

Sakamakon Bincike:

Kafar bindiddigi ta Alkalanci bayan bincike inda aka kasa samo faifan sauti inda ya fadi wadancan kalamai, kuma gidan Talabijin na Ghana suka karyata cewa ba daga gurinsu bane haka sannan shi kansa Aziz Futa ya fadi kalaman daya fada, ta yanke hukuncin cewa wannan ikirari karya ne wato Aziz Futa baiyi wadancan kalamai shiga wuta ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya da suka shafi bangarorin biyu wato bangaren Sarki Aminu Ado...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan kiyashin kiristoci a Najeriya da kuma bayanin yiwuwar turo da...

Bidiyon Nnamdi Kanu a gidan yarin Sokoto haɗin AI ne 

Bayan hukuncin da koto tayi na ɗaure Nnamdi Kanu bisa laifin ta'addanci, hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta...

Rasha da Amurka ne kan gaba wajen yaɗa labaran ƙarya a yammacin Afirka cewar Fauziyya Kabir Tukur

Shekara da shekaru ƙasashen duniya kanyi amfani da yaɗa labarai wajen yaƙi da juna ko haddasa rikici a wasu...

ƙirƙirarrayir basirar AI wanne hali Najeriya ke ciki?

A cikin watan Satumba, 2025 aka samu wani shafi na caca ya ƙirƙiri bidiyo da hoton talla na ƙarya...

Ƙarya ne: Saudiyya bata cire ɗarikar Tijjaniyya daga cikin akidu da ke da alaka da musulunci ba

Wani shafin TikTok mai suna prince hassan ya wallafa labarin cewa hukumar Saudiyya ta cire Tijjaniyya cikin jerin akidun...

Karanta wannan

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar