Kungiyar kasa da kasa ta BRICS dai a jiya laraba ta fitar da samfurin kudin kungiyar da zasu fara amfani dashi a kasuwancin kasa da kasa maimakon Dalar Amurka.
A sabon samfurin kudin dai anga tutocin kasashe da sunayen kasashe wanda ya hada da Najeriya.
Batu:
Wani mai suna Ali Suwaga Hausa 3 a wani bidiyo daya fitar mai tsawon mintuna 3 da sakan 56 a shafin TikTok yayi ikirarin cewa daga tutar kasar Rasha da ‘yan arewa sukayi shine musabbabin sanya tutar Najeriya dama rubutun Hausa.
Mun tsakuro abinda ya fada; “Akayi watsi da turanci, akayi watsi da yarabanci, akayi watsi da Ibanci, Wallahi Allah ba komai ya janyo ba kunga wannan zanga-zangar da mukai mukace a daga tutar rasha Jana’s suka daga tutar Rasha na rantse da Allah shine takai ta kawo bayan kirkiro kudin da akayi akasa Hausa kuma akasa jumhoriyar tarayyar Najeriya kuma aka makala tutar Najeriya waye yayi tunanin cewa za’a maka tutar Najeriya? Kunga shuwagabbin Najeriya a gurin? To batasu ake ba…”

Wannan bidiyo dai ya sami yadawa wato shares sama da dubu uku sannan wasu mutane sama da dubu daya suka tofa albarkacin bakin su.
Misali wani mai suna Kamal Ibrahim yace “ KO yanzU yakamata yan Nigeria mu fita mu nuna jindadinmu da faruwan wannan alkhairin asake daga tutar Russia.”

Bincike:
Cikin binciken da Alkalanci yayi shine ya gano cewa Kungiyar ta BRICS ta kara wasu kasashe 13 ciki harda Najeriya a matsayin abokan hulda (Partners) ba mambobin din-din-din ba. Kasashen sune; Algeria, Belarus, Bolivia, Cuba, Indonesia, Kazakhstan, Malaysia, Nigeria, Thailand, Turkey, Uganda, Uzbekistan, Vietnam.
A taron kungiyar ta BRICS na shekarar 2023 da akayi a kasar Afirka ta Kudu shugaba Bola Tinubu ya tura mataimkinsa a matsayin wanda ya wakilce shi wanda a wannan taro ne dai kungiyar ta bayyana cewa kasashe sama da 12 sun nuna ra’ayin shiga kungiyar.
Haka zalika ministan harkokin wajen Najeriya a wata hira da kafar jarida ta Bloomberg yace Najeriya na kawo karfin da zata iya shiga wannan kawance Ko ace kungiya.
Idan muka dawo batun rubutun jikin samfurin kudin Alkalanci ya gano cewa duk kasashen da aka rubuta sunayensu da daya daga cikin yaren kasar akayi bana turawan mulkin mallaka ba.
Misali kasar Afirka ta kudi wacce itama kasa ce da take amfani da Ingilishi a matsayin yare a gwamnatance amma bashi akayi amfani dashi ba anyi amfani da yaren kasar da akafi amfani dashi a harkokin yau da kullum a kasar.
Sakamakon Bincike:
Alkalanci dai ya gano cewa ikirarin cewa zanga-zanga tare da daga tutar Rasha ce tasa aka saka Najeriya da rubutun Hausa karya ne wato false.
Labarai masu alaka:
- Menene Hadin Kungiyar Lakurawa Da Harin Kebbi?
- Babu ‘Yan Arewa A Taron Hadin Gwiwar Najeriya Da Saudiyya?