BindiddigiMijin Rahama Sadau: ‘Yan social media na cigaba da...

Mijin Rahama Sadau: ‘Yan social media na cigaba da yada hotunan karya

-

Hukunci: Ƙarya ne
Hotunan mazaje da ake yadawa dai ba sune mijin Rahama Sadau ba hasalima binciken Alkalanci ya gano cewa wani daga ciki hotunan yana tare da ita sunanshi Comr Mahmud Muhammad. Ma’ana dai ‘yan social media sun canza masa suna zuwa Ibrahim Garba kuma sun daura masa aure da Rahama Sadau. Wani kuma abokin aikin ta ne mai suna Saleh Bala. Wani kuma hadin kirkirarriyar basirar AI ne.
Tun bayan bullar labarin auren shahararriyar ‘yar wasan kwaikwayo Rahama Sadau da wani mai suna Ibrahim Garba, hotuna ke cigaba da karade shafukan sada zumunta ana cewa ga hoton shi.
To sai dai kafar tantance labarai ta Alkalanci ta bi diddigi hotunan da ake cigaba da yadawa in da ta gano wasu bayanai da zasu baiwa masu karatu mamaki.
Da farko dai wasu sun yada wannan hoto a matsayin mijin Rahama Sadau.
Hoton karya da ake cewa shine mijin Rahama Sadau dake cigab da yaduwa
((https://www.facebook.com/share/p/14Fg7Arez98/?mibextid=wwXIfr))
To sai dai da Alkalanci tayi amfani da manhajar duba hoto na kirkirarriyar basirar AI ta gano cewa an hada mutumin da ita ne. Haka zalika an gano cewa anyi amfani da hoton Rahama Sadau data dauka a shekarar 2019 tare da abokin aikinta wajen hada wannan hoton dake cigaba da yaduwa a matsayin mijinta.
Hoton da akai amfani dashi wajen hada hoton karyar mijin Rahama Sadau
Kayan jikin sabon hoton, lallen hannun ta duka daya yake da wanda aka dauka kuma ta wallafa a shafinta na Facebook a shekarar 2019.
Na biyu kuma an wallafa wannan hoto a matsayin mijinta.
Hoton karya da ake cewa shine mijin Rahama Sadau dake cigaba da yaduwa
To sai dai binciken Alkalanci ya nuna cewa wannan hotona dake wani shirin film da tayi na turanci Wrath and Revenge.
Wannan hoto shine a farkon shafin shiri na daya na shirin fim din.
Hoto daga shafin Netflix dake nuna fim din da aka dakko hoton da ake yadawa

((https://www.netflix.com/ng/title/81520050))
Na uku an wallafa wannan hoton shima a matsayin hoton ta da mijin ta.

Hoton abokin aiki Rahama Sadau mai suna Saleh Bala da ake yadawa cewa shine mijinta

To amma akasin haka sunan shi Saleh Bala kuma daya daga cikin abokan aikin tane a gurin aiki.

Na hudu kuma wasu sun wallafa wannan hotun inda suke ikirarin cewa mijin Rahama Sadau ne.
Hoton karya da ake cewa shine mijin Rahama Sadau dake cigab da yaduwa

((https://www.facebook.com/share/p/1C5SsMDFzY/?))
To sai dai binciken Alkalanci ya gano cewa wanda ke tare da ita a hoton sunanshi Comr Mahmud Muhammad  wanda tuni ya taya Rahama Sadau murnar aure. Ma’ana dai ‘yan social media sun canza masa suna zuwa Ibrahim Garba kuma sun daura masa aure da Rahama Sadau.

Kokarin mutane na samun likes da shares da kuma na mutane dake son ganin waye mijin shararriyar ‘yar fim din shine yasa wasu yada wadannan hotuna karya wanda wasu sun sami likes da comments dubunnai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya da suka shafi bangarorin biyu wato bangaren Sarki Aminu Ado...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan kiyashin kiristoci a Najeriya da kuma bayanin yiwuwar turo da...

Bidiyon Nnamdi Kanu a gidan yarin Sokoto haɗin AI ne 

Bayan hukuncin da koto tayi na ɗaure Nnamdi Kanu bisa laifin ta'addanci, hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta...

Rasha da Amurka ne kan gaba wajen yaɗa labaran ƙarya a yammacin Afirka cewar Fauziyya Kabir Tukur

Shekara da shekaru ƙasashen duniya kanyi amfani da yaɗa labarai wajen yaƙi da juna ko haddasa rikici a wasu...

ƙirƙirarrayir basirar AI wanne hali Najeriya ke ciki?

A cikin watan Satumba, 2025 aka samu wani shafi na caca ya ƙirƙiri bidiyo da hoton talla na ƙarya...

Ƙarya ne: Saudiyya bata cire ɗarikar Tijjaniyya daga cikin akidu da ke da alaka da musulunci ba

Wani shafin TikTok mai suna prince hassan ya wallafa labarin cewa hukumar Saudiyya ta cire Tijjaniyya cikin jerin akidun...

Karanta wannan

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar