BindiddigiLabarin tilasta matasan Najeriya shiga soja ƙarya ne

Labarin tilasta matasan Najeriya shiga soja ƙarya ne

-

Hukunci: Ƙarya ne
La'akari da kasa samun wannan labari a sahihan kafafen yaɗa labarai, ƙaryata wannan labari da shalkwatar rundunar sojin ƙasa tayi bayan Alkalanci ta tuntubi mai magana da yawun rundunar, tare da tabbacin cewa shugaban bai faɗi iƙirarin tilasta matasa shiga soji ba yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa iƙirarin dake yaɗuwa na cewa shugaban rundunar sojin ƙasa ta Najeriya yace idan matasa suka ƙi shiga aikin, za a tilasta su ƙarya ne.
Akwai wani iƙirari dake yaɗuwa a kafafen sada zumunta mataƙa kan hafsan sojin ƙasa na Najeriya Laftanal Janar Waidi Shaibu.
Iƙirari:
Wani shafin Facebook mai suna Muhammad T Shehu ya wallafa iƙirarin cewa; “Shugaban Hafsan sojin Najeriya yace idan matasa sun ƙi shiga aikin, zasu wajabta wa duk wanda ya haura shekaru 18+ shiga aikin sojan….
labarin karya dake yaduwa
Wanna wallafa ta sami shares da comments da dama.
Wani shafin Facebook mai suna Wakiliya shima ya wallafa irin wannan iƙirarin.
A shafin na Wakiliya dubban mutane sun tofa albarkacin bakinsu wasu kuma sun ƙara wallafawa wato shares.
labarin karya dake yaduwa
Bincike:
Najeriya dai na fama da matsalar tsaro wanda hukumomin tsaron ke ƙoƙarin ƙara yawan dakaru.
Kafar tantance labarai ta Alkalanci ta turawa mai magana da yawun shalkwatar sojin Najeriya Laftanal Kanal Anele inda tace labarin ƙarya ne kuma abu ne da bazai iya faruwa ba.
Sannan Alkalanci ta tuntuɓi ƴan jaridar dake kawo rahoton tsaro da kuma labaran dake da alaƙa da soji inda suka tabbatar da cewa basu sami wani labarin manema labarai ko jawabi daga bakin shugaban sojin ƙasa na Najeriya.
Har ila yau Alkalanci ta gano cewa shugaban sojan ƙasa na Najeriya ya bayyana aniyar ɗaukar ƙarin sojoji 24,000. Ya faɗi hakan ne a ranar Laraba 19-11-2025 a Kaduna. Da Alkalanci ta tuntuɓi ƴan jaridar dake Kaduna sun bayyana cewa baya ga batun ɗaukar ƙarin soji shugaban rundunar soji bai faɗi batun tilasta matasa shiga soji ba.
Alkalanci ta ƙara da duba kundin tsarin mulkin Najeriya inda babu inda ya bayyana halascin tilasta wani ko wata shiga aikin soji.
Sakamakon bincike:
La’akari da kasa samun wannan labari a sahihan kafafen yaɗa labarai, ƙaryata wannan labari da shalkwatar rundunar sojin ƙasa tayi bayan Alkalanci ta tuntubi mai magana da yawun rundunar, tare da tabbacin cewa shugaban bai faɗi iƙirarin tilasta matasa shiga soji ba, yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa iƙirarin dake yaɗuwa na cewa shugaban rundunar sojin ƙasa ta Najeriya yace idan matasa suka ƙi shiga aikin, za a tilasta su ƙarya ne.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya da suka shafi bangarorin biyu wato bangaren Sarki Aminu Ado...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan kiyashin kiristoci a Najeriya da kuma bayanin yiwuwar turo da...

Bidiyon Nnamdi Kanu a gidan yarin Sokoto haɗin AI ne 

Bayan hukuncin da koto tayi na ɗaure Nnamdi Kanu bisa laifin ta'addanci, hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta...

Rasha da Amurka ne kan gaba wajen yaɗa labaran ƙarya a yammacin Afirka cewar Fauziyya Kabir Tukur

Shekara da shekaru ƙasashen duniya kanyi amfani da yaɗa labarai wajen yaƙi da juna ko haddasa rikici a wasu...

ƙirƙirarrayir basirar AI wanne hali Najeriya ke ciki?

A cikin watan Satumba, 2025 aka samu wani shafi na caca ya ƙirƙiri bidiyo da hoton talla na ƙarya...

Ƙarya ne: Saudiyya bata cire ɗarikar Tijjaniyya daga cikin akidu da ke da alaka da musulunci ba

Wani shafin TikTok mai suna prince hassan ya wallafa labarin cewa hukumar Saudiyya ta cire Tijjaniyya cikin jerin akidun...

Karanta wannan

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar