BindiddigiLabarin tilasta matasan Najeriya shiga soja ƙarya ne

Labarin tilasta matasan Najeriya shiga soja ƙarya ne

-

Hukunci: Ƙarya ne
La'akari da kasa samun wannan labari a sahihan kafafen yaɗa labarai, ƙaryata wannan labari da shalkwatar rundunar sojin ƙasa tayi bayan Alkalanci ta tuntubi mai magana da yawun rundunar, tare da tabbacin cewa shugaban bai faɗi iƙirarin tilasta matasa shiga soji ba yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa iƙirarin dake yaɗuwa na cewa shugaban rundunar sojin ƙasa ta Najeriya yace idan matasa suka ƙi shiga aikin, za a tilasta su ƙarya ne.
Akwai wani iƙirari dake yaɗuwa a kafafen sada zumunta mataƙa kan hafsan sojin ƙasa na Najeriya Laftanal Janar Waidi Shaibu.
Iƙirari:
Wani shafin Facebook mai suna Muhammad T Shehu ya wallafa iƙirarin cewa; “Shugaban Hafsan sojin Najeriya yace idan matasa sun ƙi shiga aikin, zasu wajabta wa duk wanda ya haura shekaru 18+ shiga aikin sojan….
labarin karya dake yaduwa
Wanna wallafa ta sami shares da comments da dama.
Wani shafin Facebook mai suna Wakiliya shima ya wallafa irin wannan iƙirarin.
A shafin na Wakiliya dubban mutane sun tofa albarkacin bakinsu wasu kuma sun ƙara wallafawa wato shares.
labarin karya dake yaduwa
Bincike:
Najeriya dai na fama da matsalar tsaro wanda hukumomin tsaron ke ƙoƙarin ƙara yawan dakaru.
Kafar tantance labarai ta Alkalanci ta turawa mai magana da yawun shalkwatar sojin Najeriya Laftanal Kanal Anele inda tace labarin ƙarya ne kuma abu ne da bazai iya faruwa ba.
Sannan Alkalanci ta tuntuɓi ƴan jaridar dake kawo rahoton tsaro da kuma labaran dake da alaƙa da soji inda suka tabbatar da cewa basu sami wani labarin manema labarai ko jawabi daga bakin shugaban sojin ƙasa na Najeriya.
Har ila yau Alkalanci ta gano cewa shugaban sojan ƙasa na Najeriya ya bayyana aniyar ɗaukar ƙarin sojoji 24,000. Ya faɗi hakan ne a ranar Laraba 19-11-2025 a Kaduna. Da Alkalanci ta tuntuɓi ƴan jaridar dake Kaduna sun bayyana cewa baya ga batun ɗaukar ƙarin soji shugaban rundunar soji bai faɗi batun tilasta matasa shiga soji ba.
Alkalanci ta ƙara da duba kundin tsarin mulkin Najeriya inda babu inda ya bayyana halascin tilasta wani ko wata shiga aikin soji.
Sakamakon bincike:
La’akari da kasa samun wannan labari a sahihan kafafen yaɗa labarai, ƙaryata wannan labari da shalkwatar rundunar sojin ƙasa tayi bayan Alkalanci ta tuntubi mai magana da yawun rundunar, tare da tabbacin cewa shugaban bai faɗi iƙirarin tilasta matasa shiga soji ba, yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa iƙirarin dake yaɗuwa na cewa shugaban rundunar sojin ƙasa ta Najeriya yace idan matasa suka ƙi shiga aikin, za a tilasta su ƙarya ne.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Ina gaskiyar labari da hotunan baiwa ƴan wasan Super Eagles gidaje da motoci

Bayan da aka kammala gasar cin kofin Nahiyar Afirka AFCON wanda Najeriya ta zo ta biyu, akwai labarai kala-kala...

Bidiyon da ake yaɗawa ba na waɗanda sukai kisan Ɗorayi bane 

Ƴan Najeriya dai na cigaba da jimami tare da Allah wadai da kisan wasu ƴan gida ɗaya su bakwai...

Hotunan samuwar makaman kariya zuwa Burkina Faso daga Rasha da China hadin AI ne

  Yayin da Rasha da ƙasar Sin ke ci gaba da tura makamai zuwa yankin Sahel, wani hoto da bidiyo...

Labarin cewa Aisha Buhari ta amince ta auri Sheikh Isa Ali Pantami ƙarya ne

Tun bayan kammala iddar tsohuwar matar shugaban kasa Muhammadu Buhari ake ta yada wasu labarai da iƙirarai kala-kala wanda...

Gwamna Abba Kabir Yusuf bai cire Mustapha Kwankwaso daga muƙaminsa ba

A ƙarshen watan Disemba ne dadi aka sami labarin cewa gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf zai sauya sheƙa...

Me yasa Amurka ta kai hari Sokoto?

Kasar Amurka ta takaddamar da hare-hare a wasu yankuna a arewacin Najeriya. Yanku nan sun hada da Arewa maso...

Karanta wannan

Ina gaskiyar labari da hotunan baiwa ƴan wasan Super Eagles gidaje da motoci

Bayan da aka kammala gasar cin kofin Nahiyar Afirka...

Bidiyon da ake yaɗawa ba na waɗanda sukai kisan Ɗorayi bane 

Ƴan Najeriya dai na cigaba da jimami tare da...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar