Fayyace abubuwaKisan ƴan jarida da sojin Isra'ila keyi a Gaza

Kisan ƴan jarida da sojin Isra’ila keyi a Gaza

-

Isra’ila ta kashe wani shahararren ɗan jaridar kafar yaɗa labarai ta Aljazeera Anas Al-Sheriff da abokan aikin sa huɗu a Gaza.

Gidan talabijin na Aljazeera ya tabbatar da kisan ma’aikatan nata biyar, ma’aikatan Aljazeera sune; Anas Al-Sherif, Ibrahim Zaher, Mohammed Qreiqeh, Moamen Aliwa, Mohammed Naufal. An kuma tabbatar da mutuwar wani ɗan jarida mai zaman kansa a harin da Isra’ilan ta kai a tantin da suke zaune a kofar shiga asibitin Al-Shifah a Gaza.
Hoton yan jaridar Aljazeera da Isra’ila ta kashe a ranar 10/8/2025
A baya dai ƙasar ta Isra’ila ta zargi Anas da cewa yana shugabantar wani sashe na ƙungiyar Hamas wanda kafin rasuwarsa ya sha musanta hakan. Haka zalika gidan talabijin na Aljazeera shima ya musanta cewa Anas na da alaƙa da ƙungiyar Hamas.
“Anas na aiki ne kawai na kawo rahoto tare da bayyana irin ta’asar da Isra’ila ke aikatawa a Gaza, kuma ya zama muryar marasa murya” a cewa Editan gidan talabijin na Aljazeera.
Hukumar kare haƙƙin ƴan jaridu ta Duniya tace akalla ƴan jaridu 192 Isra’ila ta kashe tun fara sabuwar mamaya da kisan ƙare dangi da Isra’ila daga 7 ga watan Oktoba, 2023.
Gidan talabijin na Aljazeera shi kuma ya rawaito cewa ƴan jarida da ma’aikatan gidajen jaridu 270 ne suka mutu sanadiyar yaƙin tun daga ranar bakwai ga watan Oktoba 2023.
Cikin waɗannan ƴan jarida da Isra’ila ta kashe 269 Falasdinawa ne.
Hoton rahoton yawan ‘yan jaridar da Isra’ila ta kashe a Gaza
Majalisar ɗinkin Duniya tace wannan yaƙi ya zama wanda yafi muni kuma aka kashe ƴan jarida da yawa a tarihi.
Gidan jaridar BBC na Turanci ya buƙaci Isra’ila data bada shaidun cewa Anas jagora ne a ƙungiyar Hamas amma basu bayar ba, wanda yasa BBC ƙasa tabbatar da zargin ko akasin haka.
Wannan dai ba shine karo na farko da Isra’ila ke kashe ƴan jarida ba a Gaza.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Ina gaskiyar labari da hotunan baiwa ƴan wasan Super Eagles gidaje da motoci

Bayan da aka kammala gasar cin kofin Nahiyar Afirka AFCON wanda Najeriya ta zo ta biyu, akwai labarai kala-kala...

Bidiyon da ake yaɗawa ba na waɗanda sukai kisan Ɗorayi bane 

Ƴan Najeriya dai na cigaba da jimami tare da Allah wadai da kisan wasu ƴan gida ɗaya su bakwai...

Hotunan samuwar makaman kariya zuwa Burkina Faso daga Rasha da China hadin AI ne

  Yayin da Rasha da ƙasar Sin ke ci gaba da tura makamai zuwa yankin Sahel, wani hoto da bidiyo...

Labarin cewa Aisha Buhari ta amince ta auri Sheikh Isa Ali Pantami ƙarya ne

Tun bayan kammala iddar tsohuwar matar shugaban kasa Muhammadu Buhari ake ta yada wasu labarai da iƙirarai kala-kala wanda...

Gwamna Abba Kabir Yusuf bai cire Mustapha Kwankwaso daga muƙaminsa ba

A ƙarshen watan Disemba ne dadi aka sami labarin cewa gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf zai sauya sheƙa...

Me yasa Amurka ta kai hari Sokoto?

Kasar Amurka ta takaddamar da hare-hare a wasu yankuna a arewacin Najeriya. Yanku nan sun hada da Arewa maso...

Karanta wannan

Ina gaskiyar labari da hotunan baiwa ƴan wasan Super Eagles gidaje da motoci

Bayan da aka kammala gasar cin kofin Nahiyar Afirka...

Bidiyon da ake yaɗawa ba na waɗanda sukai kisan Ɗorayi bane 

Ƴan Najeriya dai na cigaba da jimami tare da...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar