BindiddigiNishadiIna Gaskiyar Wakar Naziru Ta Zagin Rarara?

Ina Gaskiyar Wakar Naziru Ta Zagin Rarara?

-

Makawakin siyasa a Najeriya Rarara ya kasance mutumin da ake ta ambata a shafukan sada zumunta  tun bayan hirarsa da kafar DCL Hausa inda yayi magana kan rikicin shugabanin Najeriya da Nijar.

Batu:

Wani shafin Tiktok mai suna @abdou.salam.absi2 ya wallafa wani faifan bidiyo a ranar 5/1/2025 inda akaga mawakin nan Naziru sarkin waka kuma aka rubuta “New song by sarkin waka 🎶”
Hoton bidiyon dake cigaba da yaduwa.
Hoton bidiyon dake cigaba da yaduwa.
Wani shafin na Tiktok mai suna @binta56905 ya wallafa wannan (archived here) waka da bidiyo a ranar ta 5/1/2025.
Hoton bidiyon dake cigaba da yaduwa.
Hoton bidiyon dake cigaba da yaduwa.

Bincike:

Kafar bindiddigi da bincike ta Alkalanci ta tuntubi wani dan jarida dake aiki da gidan Talabijin na Arewa24 wanda ke gabatar da shirin fitattun wakoki Abubakar Habib Ibrahim inda yace; “ wannan ba Naziru Sarkin waka bane, domin duk da muryar ta danyi kama amma ba shi bane. Idan ka kula da kyau yanayin bakin Nazirun a wannan bidiyo bai hau wakar ba.”
Sannan kafar Alkalanci ta duba shafin Tiktok da Instagram na Naziru Sarkin waka amma bata sami wannan bidiyo ko wakar ba.

Sakamakon Bincike: 

Bisa kasa samun wakar a shafukan Naziru Sarkin waka da kuma bayanin dan jarida mai gabatar da shiri dangane da wakoki Abubakar Habib Ibrahim yasa kafar bindiddigi ta Alkalanci ta yanke hukuncin cewa wannan iƙirari ƙarya ne.

Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Shin Nijar ta rabu da Faransanci?

Tun bayan labarin amincewa da kuma ayyana Hausa a matsayin harshen kasa mutane ke ta wallafa labarin cewa Nijar...

Labaran ƙarya ne ke haddasa ƙiyayya tsakanin ‘yan kudu da ‘yan arewa

Shekara da shekaru dai ana samun rasa rayuka da dukiyoyin al’ummar arewacin Najeriya a kudancin kasar. Abubuwan da suka...

Labaran karya daga Burkina Faso na cigaba da yaduwa a Najeriya

  Da dama daga ‘yan Najeriya masu amfani da kafafen sada zumunta na cin karo da labarai kala-kala dangane da...

Najeriya-Saudiyya sun karyata labarin cewa za’a hana ‘yan kasar bizar shiga Saudiyya

Ma’aikatar harkokin wajen Najeriya ta karyata ikirarin karya da ke yawo a kafafen sadarwa na zamani, wanda ke cewa...

Ina gaskiyar cewa Amurka, Faransa ke neman haddasa faɗa tsakanin Sudan da Chadi?

  Duk lokacin da aka sami wata hatsaniya ko rikici tsakanin kasashe, wasu na amfani da wannan dama wajen yada...

Bidiyon ƴan sanda sunyi kame a Edo ƙarya ne, bidiyon ya faru a Ghana ne

  A yayin da ƴan Najeriya ke cigaba da Allah wadai da kisan wasu matafiya a jihar Edo, wasu na...

Karanta wannan

Shin Nijar ta rabu da Faransanci?

Tun bayan labarin amincewa da kuma ayyana Hausa a...

Labaran ƙarya ne ke haddasa ƙiyayya tsakanin ‘yan kudu da ‘yan arewa

Shekara da shekaru dai ana samun rasa rayuka da...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar