BindiddigiIna gaskiyar cewa Amurka, Faransa ke neman haddasa faɗa...

Ina gaskiyar cewa Amurka, Faransa ke neman haddasa faɗa tsakanin Sudan da Chadi?

-

Hukunci: Ƙarya ne
Bisa yadda Sudan ke zargin Chadi da marawa ‘yan tawayen RSF baya, wanda ya kai Sudan ta kai karar Chadi kungiyar AU kan baiwa RSF makamai. Amurka da Faransa dai basa cikin kasashen dake rura wutar rikicin Sudan. Kuma babu wani sihihin bayani da ya nuna hakan. Ya sa Alkalanci cewa wancan ikirari na cewa Amurka da Faransa ke son haddasa yiki tsakanin Sudan da Chadi karya ne.

 

Duk lokacin da aka sami wata hatsaniya ko rikici tsakanin kasashe, wasu na amfani da wannan dama wajen yada jita-jita da labaran karya.
Iƙirari:
Akwai wani shafin kafar sada zumunta na TikTok mai suna @zilaihatmustafa2 (Ali Suwaga Hausa 2) ya wallafa wani faifan bidiyo mai tsawon mintuna bakwai da sakan takwas a ranar 29-03-2025, inda maimagana a cikin bidiyon yake iƙirarin cewa ƙasashen Amurka da Faransa ke son haddasa yaƙi tsakanin Sudan da Chadi.
Bincike:
Taƙaddama tsakanin ƙasar Sudan da Chadi dai ta kwana biyu ana yi. Gwamnatin Sudan dama wasu jami’an Majalisar Ɗinkin Duniya sun sha zargin Chadi da goyawa ƴan tawayen RSF baya.
Galibin dakarun RSF dai mutanen yankin Darfur ne wanda tun fil azal  al’umomin yankin Darfur ƴan uwan juna ne da makwabtansu da ke gabashin Chadi.
Gwamnatin Sudan ta daɗe tana gargaɗin gwamnatin Chadi da ta daina taimakawa mayaƙan RSF, ƙasar ta Chadi ta musanta.
A kwanakin baya ma dai wani babban jami’in gwamnatin Sudan ya yi barazanar kai wa Chadi hari a cewar sa idan har “ba ta daina tallafawa abokan gaban Sudan ba wato RSF.”
A ɓangaren Chadi kuwa wani babban sojan ƙasar Birgediya Janar Acheikh Issakha Acheikh ya bayyana shirin dakarun ƙasar na kare ta, kuma ya sha alwashin kai wa Sudan martani da ya dace na hare-hare.
A Nuwanban shekarar 2024 sai da ministan  Shari’ar kasar ta Sudan Muawiya Osman ya ce gwamnatin Burhan ta kai karar kasar Chadi gaban kungiyar Tarayyar Afirka.
Da yake magana da manema labarai, ciki har da AFP, Osman ya ce gwamnati ta buƙaci a biya ta diyya, ya kuma zargi Chadi da “sayar da makamai ga mayakan ‘yan tawaye” da kuma “illata ‘yan kasar Sudan”.
Tuni dai sojojin ƙasar ta Sudan suka kwace babban birnin ƙasar Khartoum da wasu garuruwa dake kewaye daga hannun mayaƙan RSF.
Sakamakon binciken:
Bisa la’akari da alaƙar da takun sakar dake tsakanin shugabannin Sudan da na Chadi kan batun zargin taimakawa ƴan tawayen RSF, dama kai karar Chadi zuwa Kungiyar Tarayyar Afrika AU, da kuma samun musayar yawu tsakanin ƙasashen biyu yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa iƙirarin cewa Amurka da Faransa na da hannu ƙarya ne.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa wani labari tare da hotuna wanda ya yadu matuka da...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da suka bayyana cewa ‘yan Najeriya sunyi asarar makudan kudade yayin...

Cirani: Shin Tarayyar Turai ta amince ‘yan Afrika su tsallaka ta Libya ba tare da Biza ba?

Duk da cewa kasashen turai na nuna damuwa tare da daukar matakan rage shigar bakin haure, ‘yan cirani dake...

Shin Nijar ta rabu da Faransanci?

Tun bayan labarin amincewa da kuma ayyana Hausa a matsayin harshen kasa mutane ke ta wallafa labarin cewa Nijar...

Labaran ƙarya ne ke haddasa ƙiyayya tsakanin ‘yan kudu da ‘yan arewa

Shekara da shekaru dai ana samun rasa rayuka da dukiyoyin al’ummar arewacin Najeriya a kudancin kasar. Abubuwan da suka...

Labaran karya daga Burkina Faso na cigaba da yaduwa a Najeriya

  Da dama daga ‘yan Najeriya masu amfani da kafafen sada zumunta na cin karo da labarai kala-kala dangane da...

Karanta wannan

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar