BindiddigiIna Gaskiyar Cewa Akpabio Ya Ba Wa Natasha Hakuri

Ina Gaskiyar Cewa Akpabio Ya Ba Wa Natasha Hakuri

-

A cikin ‘yan makwannin nan dai an sami cacar baki tare da zarge-zarge tsakanin shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio da Sanata Natasha Akpoti, wanda yanzu haka aka fara samun yaduwar labaran karya akan takaddamar.

Ikirari:

Akwai dai wani labarin dake yaduwa a kafar sada zumunta ta Facebook sosai inda wasu ke ikirarin shugaban majalisar dattawan Najeriya Godswill Akpabio ya ba wa Sanata Natasha Akpoti hakuri kan abinda ya faru a tsakanin su cikin ‘yan kwanakin nan.
Misalin shafi mai suna ATP Hausa ya wallafa wani bidiyo a ranar 02/03/2025, tare da rubuta cewa “ Ina Mai Baiwa Sanata Natasha Hakuri A Kan Rashin Fahimtar Da Ya Faru Tsakanina Da Ita, Duk Abinda Na Yi Mata bataji dadi ba Ta Yi Hakuri – Shugaban Majalisar Dattijai, Sanata Akpabio”

Wannan wallafa ta sami mutane dabunnai da suka kalla.

Hoton ikirarin karya dake cigaba da yaduwa.
Hoton ikirarin karya dake cigaba da yaduwa.
Wani shafi ma mai suna Jaridar Arewa ya wallafa bidiyon ranar 02/03/2025 inda aka rubuta cewa; “Ina Mai Baiwa Sanata Natasha Hakuri A Kan Rashin Fahimtar Da Ya Faru Tsakanina Da Ita, Duk Abinda Na Yi Mata bataji dadi ba Ta Yi Hakuri – Shugaban Majalisar Dattijai, Sanata Akpabio.”
Wannan wallafa ta sami mutane sama da dubu hudu da suka kalla cikin kasa da awa biyu da wallafawa.
Hoton ikirarin karya dake cigaba da yaduwa.
Hoton ikirarin karya dake cigaba da yaduwa.
Wani shafin shima mai suna Daily Reports Hausa ya wallafa hoto dake dauke da Sanata Akpabio da Sanata Natasha inda ya rubuta cewa, “ Ina Mai Baiwa Sanata Natasha Hakuri A Kan Rashin Fahimtar Da Ya Faru Tsakanina Da Ita, Duk Abinda Na Yi Mata bataji dadi ba Ta Yi Hakuri – Shugaban Majalisar Dattijai, Sanata Akpabio.”
Hoton ikirarin karya dake cigaba da yaduwa.
Hoton ikirarin karya dake cigaba da yaduwa.

Bincike:

Kafar tantance labarai, bindiddigi da bincike ta Alkalanci ta duba bidiyo bada hakurin da akaji Sanata Akpabio na ba wa Sanata Natasha ya faru ne watanni bakwai da suka gabata wato a ranar 23/07/2024 yayin zaman majalisar.
Bidiyon dai wanda ke yaduwa shine wanda gidan Talabijin na Channels ya wallafa a shafin YouTube dinsa watanni bakwai da suka wuce wanda ya sami mutane da suka kalla sama da dubu dari da sittin.
A bidiyon da ke yaduwa dai anji Sanata Akpabio yana bayyana cewa yayi nadamar fadin kalamai na cewa a gidan gala ake daga murya, wanda wadannan maganganu basu yiwa mutane da dama da ita kanta Sanata Natasha dadi ba. Ya ce shima yana da uwargida kuma ya na da ‘ya’ya mata  bazaiso wani yaci zarafin su ko kuma dakile kokarin su na zama wani abu ba.
kafar jaridar BBC pidgin ma ta wallafa labarin a ranar 23/07/2024.

Haka zalika babu wata gidan jarida sahihiya da ta rawaito wannan labari a matsayin sabon labari daya faru.

Sakamakon bincike:

Baya ga samo asalin lokacin da akai bidiyon da ake yadawa yanzu na bada hakuri da kuma kalaman shugaban majalisar dattawan Godswill Akpabio wanda yake bada hakuri kan batun kalamansa na gidan gala ga iya Sanata Natasha. Sannan ganin cewa bidiyon da kalaman tsofaffi ne kuma basu da alaka da sabuwar takadda tsakanin Sanatocin biyu yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa wannan ikirari karya ne.
Labarai masu alaka: 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya da suka shafi bangarorin biyu wato bangaren Sarki Aminu Ado...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan kiyashin kiristoci a Najeriya da kuma bayanin yiwuwar turo da...

Bidiyon Nnamdi Kanu a gidan yarin Sokoto haɗin AI ne 

Bayan hukuncin da koto tayi na ɗaure Nnamdi Kanu bisa laifin ta'addanci, hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta...

Rasha da Amurka ne kan gaba wajen yaɗa labaran ƙarya a yammacin Afirka cewar Fauziyya Kabir Tukur

Shekara da shekaru ƙasashen duniya kanyi amfani da yaɗa labarai wajen yaƙi da juna ko haddasa rikici a wasu...

ƙirƙirarrayir basirar AI wanne hali Najeriya ke ciki?

A cikin watan Satumba, 2025 aka samu wani shafi na caca ya ƙirƙiri bidiyo da hoton talla na ƙarya...

Ƙarya ne: Saudiyya bata cire ɗarikar Tijjaniyya daga cikin akidu da ke da alaka da musulunci ba

Wani shafin TikTok mai suna prince hassan ya wallafa labarin cewa hukumar Saudiyya ta cire Tijjaniyya cikin jerin akidun...

Karanta wannan

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar