BindiddigiBidiyon ƴan sanda sunyi kame a Edo ƙarya ne,...

Bidiyon ƴan sanda sunyi kame a Edo ƙarya ne, bidiyon ya faru a Ghana ne

-

Hukunci: Ƙarya ne
Kafar tantance labarai ta Alkalanci ta gano tambarin yan sandan Ghana, da kuma lambar kira don agajin gaggawa ta Ghana a bidiyon dake yaduwa wanda ya tabbatar da cewa ba’a Edo bane.

 

A yayin da ƴan Najeriya ke cigaba da Allah wadai da kisan wasu matafiya a jihar Edo, wasu na amfani da wannan dama wajen yaɗa labarai, hotuna da bidiyon ƙarya kan abun.
Iƙirari:
Wani shafin Facebook mai suna Abumusa’ab J Aliyu ya wallafa wani rubuta da faifan bidiyo dake cewa
“Hukumomi Sun Fara Kama Matsiyatan da Suka Yiwa Yan Uwanmu Hausawa Matafiya Kisan Gilla A Jihar Edo…”
Hoton bidiyon karya dake cigaba da yaduwa
Shima wani shafin na facebook mai suna Nasiru Ibrahim Babajo ya wallafa irin wannan bidiyo inda ya rubuta cewa;
“Alhamdulillah An cigaba da kama yan lskan da suka yiwa Yan Arewa k!ssan gilla a Jihar Edo.”
Hoton post din karya dake cigaba da yaduwa
Bincike:
Kafar tantance labarai, bindiddigi da bincike ta Alkalanci ta duba shafin rundunar ƴan sanda Najeriya inda ta tabbatar da kama mutum goma sha huɗu da ake zargi da hannu wajen kisan to amma babu hoto ko bidiyo.
Alkalanci ta duba wannan bidiyo da idon basira tare da gano tambarin ƴan sanda ƙasar Ghana a jikin rigunan ƴan sandan.
Haka zalika a jikin motar ƴan sandan an  rubuta lambar 191 da 18555 waɗanda lambobin kiran ƴan sanda domin agajin gaggawa na ƙasar Ghana ne.
Hoton sashen dake nuna lambar yan sandan Ghana a bidiyon
Lambar kira domin agajin gaggawa a Najeriya 112 ce.
Sakamakon bincike:
Bisa la’akari da kayan ƴan sanda da aka gani a bidiyon, tambarin dake ɗauke da Ghana, da kuma lambar neman agajin ƴan sandan ƙasar Ghana a jikin motar ƴan sandan yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa iƙirarin cewa bidiyon kame ne da ƴan sandan Nijeriya sukayi a Edo ƙarya ne.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Shin da gaske akwai ‘yar tsama tsakanin Tinubu da Kashim?

Tun bayan dawowar damakradiyya a shekarar 1999 za’a iya cewa samun rashin jituwa tsakanin shugaban kasa da mataimakinsa ba...

Waɗanne ƙasashe ake ganin suna goyon bayan kafa gwamnatin ƴan tawaye a Sudan?

Ayyana gwamnatin ƴan tawaye da jagoran RSF Laftanar-Janar Mohamed Hamdan Dagalo ya yi a Sudan, ya zo a daidai lokacin...

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa wani labari tare da hotuna wanda ya yadu matuka da...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da suka bayyana cewa ‘yan Najeriya sunyi asarar makudan kudade yayin...

Cirani: Shin Tarayyar Turai ta amince ‘yan Afrika su tsallaka ta Libya ba tare da Biza ba?

Duk da cewa kasashen turai na nuna damuwa tare da daukar matakan rage shigar bakin haure, ‘yan cirani dake...

Shin Nijar ta rabu da Faransanci?

Tun bayan labarin amincewa da kuma ayyana Hausa a matsayin harshen kasa mutane ke ta wallafa labarin cewa Nijar...

Karanta wannan

Shin da gaske akwai ‘yar tsama tsakanin Tinubu da Kashim?

Tun bayan dawowar damakradiyya a shekarar 1999 za’a iya...

Waɗanne ƙasashe ake ganin suna goyon bayan kafa gwamnatin ƴan tawaye a Sudan?

Ayyana gwamnatin ƴan tawaye da jagoran RSF Laftanar-Janar Mohamed Hamdan...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar