BindiddigiBidiyon ƴan sanda sunyi kame a Edo ƙarya ne,...

Bidiyon ƴan sanda sunyi kame a Edo ƙarya ne, bidiyon ya faru a Ghana ne

-

Hukunci: Ƙarya ne
Kafar tantance labarai ta Alkalanci ta gano tambarin yan sandan Ghana, da kuma lambar kira don agajin gaggawa ta Ghana a bidiyon dake yaduwa wanda ya tabbatar da cewa ba’a Edo bane.

 

A yayin da ƴan Najeriya ke cigaba da Allah wadai da kisan wasu matafiya a jihar Edo, wasu na amfani da wannan dama wajen yaɗa labarai, hotuna da bidiyon ƙarya kan abun.
Iƙirari:
Wani shafin Facebook mai suna Abumusa’ab J Aliyu ya wallafa wani rubuta da faifan bidiyo dake cewa
“Hukumomi Sun Fara Kama Matsiyatan da Suka Yiwa Yan Uwanmu Hausawa Matafiya Kisan Gilla A Jihar Edo…”
Hoton bidiyon karya dake cigaba da yaduwa
Shima wani shafin na facebook mai suna Nasiru Ibrahim Babajo ya wallafa irin wannan bidiyo inda ya rubuta cewa;
“Alhamdulillah An cigaba da kama yan lskan da suka yiwa Yan Arewa k!ssan gilla a Jihar Edo.”
Hoton post din karya dake cigaba da yaduwa
Bincike:
Kafar tantance labarai, bindiddigi da bincike ta Alkalanci ta duba shafin rundunar ƴan sanda Najeriya inda ta tabbatar da kama mutum goma sha huɗu da ake zargi da hannu wajen kisan to amma babu hoto ko bidiyo.
Alkalanci ta duba wannan bidiyo da idon basira tare da gano tambarin ƴan sanda ƙasar Ghana a jikin rigunan ƴan sandan.
Haka zalika a jikin motar ƴan sandan an  rubuta lambar 191 da 18555 waɗanda lambobin kiran ƴan sanda domin agajin gaggawa na ƙasar Ghana ne.
Hoton sashen dake nuna lambar yan sandan Ghana a bidiyon
Lambar kira domin agajin gaggawa a Najeriya 112 ce.
Sakamakon bincike:
Bisa la’akari da kayan ƴan sanda da aka gani a bidiyon, tambarin dake ɗauke da Ghana, da kuma lambar neman agajin ƴan sandan ƙasar Ghana a jikin motar ƴan sandan yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa iƙirarin cewa bidiyon kame ne da ƴan sandan Nijeriya sukayi a Edo ƙarya ne.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Ina gaskiyar labari da hotunan baiwa ƴan wasan Super Eagles gidaje da motoci

Bayan da aka kammala gasar cin kofin Nahiyar Afirka AFCON wanda Najeriya ta zo ta biyu, akwai labarai kala-kala...

Bidiyon da ake yaɗawa ba na waɗanda sukai kisan Ɗorayi bane 

Ƴan Najeriya dai na cigaba da jimami tare da Allah wadai da kisan wasu ƴan gida ɗaya su bakwai...

Hotunan samuwar makaman kariya zuwa Burkina Faso daga Rasha da China hadin AI ne

  Yayin da Rasha da ƙasar Sin ke ci gaba da tura makamai zuwa yankin Sahel, wani hoto da bidiyo...

Labarin cewa Aisha Buhari ta amince ta auri Sheikh Isa Ali Pantami ƙarya ne

Tun bayan kammala iddar tsohuwar matar shugaban kasa Muhammadu Buhari ake ta yada wasu labarai da iƙirarai kala-kala wanda...

Gwamna Abba Kabir Yusuf bai cire Mustapha Kwankwaso daga muƙaminsa ba

A ƙarshen watan Disemba ne dadi aka sami labarin cewa gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf zai sauya sheƙa...

Me yasa Amurka ta kai hari Sokoto?

Kasar Amurka ta takaddamar da hare-hare a wasu yankuna a arewacin Najeriya. Yanku nan sun hada da Arewa maso...

Karanta wannan

Ina gaskiyar labari da hotunan baiwa ƴan wasan Super Eagles gidaje da motoci

Bayan da aka kammala gasar cin kofin Nahiyar Afirka...

Bidiyon da ake yaɗawa ba na waɗanda sukai kisan Ɗorayi bane 

Ƴan Najeriya dai na cigaba da jimami tare da...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar