Fayyace abubuwaAbinda muka sani dangane da Laftanar A.M Yerima

Abinda muka sani dangane da Laftanar A.M Yerima

-

Tun bayan sa-in-sa da aka samu tsakanin Laftanar Yerima da Nyesom Wike a Abuja, ake ta yamaɗiɗin cewa wannan matashin soja ɗa ne ga Birgediya Janar Mohammed M Yerima mai ritaya.

Wani shafin Facebook mai suna Mikiya ya wallafa wannan labari wanda mutane sama da dubu daya da dari shida suka tofa albarkacin baki, yayin da sama da dubu daya da dari biyu suka kara wallafawa wato shares.

Labarin da babu sahihanci dake yaduwa

Sunansa Laftanar Ahmed Yerima, sojan ruwa ne wanda aka haifa a Kaduna kuma ya girma a Kaduna da kuma Fatakwal na jihar Rivers, duk da cewa iyayensa  ‘yan asalin garin Fune ne da ke jihar Yobe.

A shekarar 2011 ne Ahmed Yarima, mai shekaru 33 da haihuwa ya fara karatu a sashen koyar da aikin jarida a jami’ar Ahmadu Bello da ke Zaria.

Amma bai kammala karatu a ABU ba domin Yerima ya bar jami’ar Ahmadu Bello bayan shekara ɗaya bayan ya sami gurbi a NDA da ke Kaduna a 2012.

Yerima ya fito a matsayin Laftanar na sojan ruwa a shekarar 2017.

Menene hadin sojojin biyu?

Sahihan bayanai sun tabattar da cewa sojojin biyu sun fito ne daga jiha ɗaya, wato jihar Yobe, to amma akwai bambancin gari.

Birgediya Janar Mohammed M. Yerima mai ritaya wanda tsohon mai magana da yawun rudunar sojan kasar Najeriya ne, ya fito daga ƙaramar hukumar Bade, yayin da Laftanar A.M Yarima ya fito daga ƙaramar hukumar Fune.

Sai dai bayan dogon bincike da BBC  da kuma jaridar PRNigeria suka gudanar, sun gano cewa wannan iƙirari ba gaskiya ba ne.

Binciken kuma ya tabbatar da mahaifin wannan matashin Laftanal A.M Yerima ba soja ba ne, harkokin kasuwanci yayi yayin rayuwarsa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Ina gaskiyar Iƙirarin mai da waɗanda ake zargi da kisa a Kano zuwa kudancin Najeriya?

IƙirariWani bidiyo yana ta yaɗuwa a kafar sada zumunta ta TikTok wanda ke nuna cewa jami'an tsaro sun kwashe...

Ina gaskiyar labari da hotunan baiwa ƴan wasan Super Eagles gidaje da motoci

Bayan da aka kammala gasar cin kofin Nahiyar Afirka AFCON wanda Najeriya ta zo ta biyu, akwai labarai kala-kala...

Bidiyon da ake yaɗawa ba na waɗanda sukai kisan Ɗorayi bane 

Ƴan Najeriya dai na cigaba da jimami tare da Allah wadai da kisan wasu ƴan gida ɗaya su bakwai...

Hotunan samuwar makaman kariya zuwa Burkina Faso daga Rasha da China hadin AI ne

  Yayin da Rasha da ƙasar Sin ke ci gaba da tura makamai zuwa yankin Sahel, wani hoto da bidiyo...

Labarin cewa Aisha Buhari ta amince ta auri Sheikh Isa Ali Pantami ƙarya ne

Tun bayan kammala iddar tsohuwar matar shugaban kasa Muhammadu Buhari ake ta yada wasu labarai da iƙirarai kala-kala wanda...

Gwamna Abba Kabir Yusuf bai cire Mustapha Kwankwaso daga muƙaminsa ba

A ƙarshen watan Disemba ne dadi aka sami labarin cewa gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf zai sauya sheƙa...

Karanta wannan

Ina gaskiyar Iƙirarin mai da waɗanda ake zargi da kisa a Kano zuwa kudancin Najeriya?

IƙirariWani bidiyo yana ta yaɗuwa a kafar sada zumunta...

Ina gaskiyar labari da hotunan baiwa ƴan wasan Super Eagles gidaje da motoci

Bayan da aka kammala gasar cin kofin Nahiyar Afirka...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar