BindiddigiIkirarin karya kan mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shettima

Ikirarin karya kan mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shettima

-

Hukunci: Ƙarya ne
Kasancewar babu wata kafar yada labarai sahihiya da ta rawaito labarin, kuma babu faifon bidiyo ko sauti da ya nuna mataimakin shugaban kasa yayi wadancan kalamai. Haka zalika mai magana da yawun sa ya musanta hakan tare da cewa tun watan Janairu ake yada wancan labari a harshen Turancin Ingilishi ya sa Alkalanci yanke hukuncin cewa labarin karya ne.

Ikirari:

Wani shafin Facebook mai suna DDL Hausa ya wallafa wani ikirari dake cewa mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya koka kan yadda dan gidan shugaban kasa Seyi Tinubu ke masa shisshigi:
“Shishshiginka yayi yawa Kabarni Nayi Aikina Tunda Ba kaine kanaɗa Ni a matsayin Mataimakin shugaban ƙasa Ba, Shettima Ya Koka Kan Yunkurin Karbe iko daga Hannunsa Wanda Sheyi Tinubu yake ƙoƙarin yi a Halin yanzu. Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya bayyana damuwarsa kan abin da ya kira yunkurin kwace aikinsa, yana zargin dan Shugaba Bola Tinubu da yin ayyukan da ya kamata ya gudanar. Shettima ya ce Ban taɓa jin kaina a matsayin Mataimakin Shugaban Ƙasa ba. Duk da cewa ya kamata in gudanar da muhimman ayyuka, dan Tinubu ne yake yin aikina.”
Hoton labarin karya dake cigaba da yaduwa.
Hoton labarin karya dake cigaba da yaduwa.
Wannan ikirari dai ya sami tofa albarkacin baki wato comments sama da dari hudu tare da shares sama da dari uku.
Wani shafin na Facebook mai suna Gida-Gida TV shima ya wallafa irin wannan post a ranar 22/03/2025.
Shima shafin Gida-Gida TV ya sami comments sama da dari .
Hoton labarin karya dake cigaba da yaduwa.
Hoton labarin karya dake cigaba da yaduwa.

Bincike:

Kafar tantance labarai, bindiddigi da bincike ta Alkalanci ta tuntubi Stanley Nkwocha mai magana da yawun mataimakin shugaban kasar Najeriya Kashim Shettima  inda yace wannan magana ta masu yada karya ce kawai.

 Haka Zalika ya bayyanawa Alkalanci cewa tun watan Janairun 2025 irin wannan ikirari ke yaduwa a harshen turanci wanda tuni sun bayyana cewa labarin karya ne.

Sannan kafar tantance labarai ta Alkalanci ta duba sahihan gidajen jaridu don duba ko akwai wacce ta wallafa makamancin wannan labarai, to sai da Alkalanci bai samo komai ba.
Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima dai ya sha wakiltar shugaban kasa Bola Tinubu a ayyukan gwamnati a ciki da wajen Najeriya.
Hotuna da labarai a sahihan kafafen yada labarai ya nuna cewa yana gudanar da ayyukan na harkokin mulki yau da kullum.
A cikin Azumin 1446AH/2025 ne dai aka ga dan shugaban kasa Seyi Tinubu na ran gadi jihohi yana shan ruwa da matasa.

Sakamakon bincike:

Bisa ka sa samo labarin a wata sahihiyar gidan jarida na cewa mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima yayi wadancan kalamai, da kuma bayanin mai magana da yawun sa, tare da samun labarai kala-kala dake nuna yadda mataimakin shugaban kasa ke ayyukan sa. Kafar tantance labarai ta Alkalanci ta yanke hukunci cewa wancan ikirari karya ne.
Labarai masu alaka:

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Ina gaskiyar Iƙirarin mai da waɗanda ake zargi da kisa a Kano zuwa kudancin Najeriya?

IƙirariWani bidiyo yana ta yaɗuwa a kafar sada zumunta ta TikTok wanda ke nuna cewa jami'an tsaro sun kwashe...

Ina gaskiyar labari da hotunan baiwa ƴan wasan Super Eagles gidaje da motoci

Bayan da aka kammala gasar cin kofin Nahiyar Afirka AFCON wanda Najeriya ta zo ta biyu, akwai labarai kala-kala...

Bidiyon da ake yaɗawa ba na waɗanda sukai kisan Ɗorayi bane 

Ƴan Najeriya dai na cigaba da jimami tare da Allah wadai da kisan wasu ƴan gida ɗaya su bakwai...

Hotunan samuwar makaman kariya zuwa Burkina Faso daga Rasha da China hadin AI ne

  Yayin da Rasha da ƙasar Sin ke ci gaba da tura makamai zuwa yankin Sahel, wani hoto da bidiyo...

Labarin cewa Aisha Buhari ta amince ta auri Sheikh Isa Ali Pantami ƙarya ne

Tun bayan kammala iddar tsohuwar matar shugaban kasa Muhammadu Buhari ake ta yada wasu labarai da iƙirarai kala-kala wanda...

Gwamna Abba Kabir Yusuf bai cire Mustapha Kwankwaso daga muƙaminsa ba

A ƙarshen watan Disemba ne dadi aka sami labarin cewa gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf zai sauya sheƙa...

Karanta wannan

Ina gaskiyar Iƙirarin mai da waɗanda ake zargi da kisa a Kano zuwa kudancin Najeriya?

IƙirariWani bidiyo yana ta yaɗuwa a kafar sada zumunta...

Ina gaskiyar labari da hotunan baiwa ƴan wasan Super Eagles gidaje da motoci

Bayan da aka kammala gasar cin kofin Nahiyar Afirka...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar