BindiddigiShin Shugaban ƙasa zai iya dakatar da gwamna?

Shin Shugaban ƙasa zai iya dakatar da gwamna?

-

Hukunci: Ƙarya ne
Kasancewar kundin tsarin mulki bai baiwa shugaban kasa da ma ba wajen dakatar da zababben gwamna. Yasa Alkalanci cewa shugaban kasa bai da hurumi.

A ranar 18 ga watan Maris na 2025 shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ayyana dokar ta ɓaci a jihar Ribas tare da dakatar da gwamna da mataimakiyar sa da ƴan majalisar dokokin jihar.

Tuni dai Tinubu ya naɗa tsohon hafsan sojin ruwa Ibok-Ete Ibas a matsayin shugaban a jihar.

Yayin jawabi ga ƴan Najeriya kan wannan mataki Tinubu yace yayi hakan ne bisa ƙarfin da sashe na 305 na kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999 ya bashi.

Akwai dai rabuwar kai tsakanin ƴan Najeriya kan wannan dakatarwa da kuma ayyana dokar ta ɓacin.
Wasu ƴan ƙasar na ganin ya sabawa doka wasu kuma na ganin shugaba Tinubu na kan dai-dai.
A shekarar 2004 shugaba Olusegun Obasanjo ya taɓa dakatar da gwamnan jihar Filato Joshua Dariye.
Sai kuma a shekarar 2006 nan ma ya dakatar da gwamnan jihar Ekiti Ayodele Fayose

Me kundin tsarin mulkin yace?

Sashe na 305 na kundin tsarin mulkin Najeriya ya baiwa shugaban ƙasa damar sanya dokar ta ɓaci idan akwai babban rikici a jiha. To sai dai wannan sashe bai baiwa shugaban ƙasa damar ko ƙarfin iya dakatar ko cire gwamna ba.
Hasali ma sashen kundin tsarin mulki na 188 da na 189 dakatar da gwamna ko cire shi aiki ne na majalisar dokokin jihar.
Haka zalika sashen na 11 (4) na kundin tsarin mulkin ya baiwa majalisar dokokin ta ƙasa da ta ɗauki ayyukan majalisar dokokin jihar idan har majalisar dokokin sun kasa ko ba zasu iya gudanar da ayyukan su ba.
Kuma tsarin mulkin Najeriya bai baiwa shugaban ƙasa damar dakatar da ayyukan majalisar dokokin jihar ba, domin kuwa yin hakan aiki ne na bangaren Shari’a da kuma majalisa ba harkar sashen zartaswa na ƙasa bane.
Kungiyar lauyoyi ta Najeriya NBA tayi Allah wadai da dakatar da zababben gwamna, mataimakiyar sa da kuma yan majalisar dokoki inda kungiyar ta bayyana hakan a matsayin haramtaccen mataki, wanda ya sabawa kundin tsarin mulkin Najeriya.
Shugaban kungiyar ta kasa Afam Osigwe SAN yace shugaban kasa bashi da hurumin dakatar da zababben gwamna, mataimakiyar gwamna da kuma zababbun ‘yan majalisar dokikin jiha.

Me doka tace kan sanya dokar ta ɓaci?

Duk da cewa kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999 ya baiwa shugaban ƙasa damar ayyana dokar ta ɓaci.
To amma dole sai ya miƙa wannan buƙata ga shugaban majalisar dattawa da na  wakilai idan ana so ta zama halattacciyar doka.
Sashe na 305 (3) wanda ya haɗa daga (a zuwa g)  ya bayyana rikicin da ka iya sanyawa a ayyana dokar ta ɓaci.
  1.  Idan ƙasa tana cikin yanayin yaƙi.
  2.  Idan ƙasa na cikin barazanar mamaya ko fadawa cikin yaƙi.
  3. Idan taɓarɓarwar doka da oda, rashin tabbas na tsaron lafiyar mutane a ƙasa ko wani sashe na ƙasa wanda dole a ɗauka mataki mai tsauri domin dawo da zaman lafiya.
  4. Idan akwai tabbacin wani haɗari na rashin bin doka da oda, wanda akwai buƙatar daƙile yiwuwar hakan.
  5. Idan haɗari, ko wani babban ibtila’i da ya sami wani yanki na ƙasa.
  6.  Idan akwai kowanne irin matsala da ka iya yin barazana ga kasancewa Najeriya dunkulalliyar ƙasa.
  7.  Idan shugaban ƙasa ya sami rokon buƙatar hakan, wanda yayi dai-dai da ƙaramin sashe na 4 cikin baka.

Sakamakon bincike:

Kasancewar duk da kundin tsarin mulki ya baiwa shugaban ƙasa damar sanya dokar ta ɓaci a jiha amma bai bashi damar dakatar da zaɓaɓɓen gwamna da majalisar dokokin jihar ba, yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa a doka shugaban ƙasa bashi da damar dakatar da zaɓaɓɓen gwamna ko majalisar dokokin jiha.
Labarai masu alaka: 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya da suka shafi bangarorin biyu wato bangaren Sarki Aminu Ado...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan kiyashin kiristoci a Najeriya da kuma bayanin yiwuwar turo da...

Bidiyon Nnamdi Kanu a gidan yarin Sokoto haɗin AI ne 

Bayan hukuncin da koto tayi na ɗaure Nnamdi Kanu bisa laifin ta'addanci, hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta...

Rasha da Amurka ne kan gaba wajen yaɗa labaran ƙarya a yammacin Afirka cewar Fauziyya Kabir Tukur

Shekara da shekaru ƙasashen duniya kanyi amfani da yaɗa labarai wajen yaƙi da juna ko haddasa rikici a wasu...

ƙirƙirarrayir basirar AI wanne hali Najeriya ke ciki?

A cikin watan Satumba, 2025 aka samu wani shafi na caca ya ƙirƙiri bidiyo da hoton talla na ƙarya...

Ƙarya ne: Saudiyya bata cire ɗarikar Tijjaniyya daga cikin akidu da ke da alaka da musulunci ba

Wani shafin TikTok mai suna prince hassan ya wallafa labarin cewa hukumar Saudiyya ta cire Tijjaniyya cikin jerin akidun...

Karanta wannan

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar