Alakar Najeriya da kasar Saudiyya dadaddiyar alaka ce musamman kasancewar shekaru aru-aru musulman Najeriya na zuwa aikin hajji da umarah dama harkokin kasuwanci.
Batu:
Akwai wani faifai sauti mai tsawon minti daya da sakan talatin da biyar hade da hoto dake yaduwa a kafar sada zumunta ta WhatsApp dake ikirarin cewa akwai wani taro na musamman (summit) tsakanin Najeriya da kasar Saudiyya kuma babu Ko dan arewa daya a cikin wadanda zasu je taron.
Kadan daga cikin abinda ake cewa a sautin; “ yallabai an tashi lafiya? Ni dai bana Najeriya for quite sometimes to amma nayi iyaka nawa, wannan summit din da za’ayi babu dan arewa Ko daya a ciki, kuma ya kamata ace mutanenmu gaskiya blame game din da ake wa yan kudu ba laifun su bane laifun mu ne, hassada da kya shi ita ta dankaremu Yanzu ace za’ayi wannan a Saudiyya mu da muke da relationship da Saudiyya tun kan Britain suzo mu arewa gashi abunda ake a business dinma anyi sidelining dinmu saboda da haka in da yadda za’ayi reaching out su manyan malamai da sukai karatu a Saudiyya Ko shi ambasada dake Saudiyya tunda shi dan arewa ne…”
Haka zalika an sami wani faifan mai tsawon mintuna biyu da sakanni goma sha uku, da yake nuna cewa maganar da wancan yayi gaskiya ne.
Bincike:
Alkalanci mun tuntubi ofishin sakataren gwamnati dama ma’aikatar harkokin waje ta Najeriya inda muka samo wata takarda da ofishin shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa Femi Gbajabiamila inda yace binciken da aka gudanar ya nuna cewa wannan taro bai sami sahalewar hukumomin kasar Saudiyya ba hasalima shugaban wata hukuma mai suna NDCC ne ke kokarin damfarar jami’an gwamnati da kamfanin sa.
Takardar da fadar shugaban kasa ta rubuta zuwa ga sakataren gwamnatin tarayya yace ofishi na ya sami takardar gayyatar shugaban kasa zuwa kasar Saudiyya domin taro da kuma bada kyautar karramawa ga shugaban Najeriya Bola Tinubu.
Takardar tace shugaban NDCC mai suna Miebaka Kenneth Adoki ne ya tura takardar gayyatar inda take cewa za’a gudanar da taron a tsakanin ranar 18 zuwa 24 ga wannan watan na Nuwamba a birnin Jidda dake Saudiyya.
A takaradar Gbajabiamila yace an gano cewa Mr. Adoki na kokarin zambatar fadar shugaban kasa ne kawai da sunan hukumar NDCC.
Sakamakon Bincike:
Sakamakon binciken Alkalanci ya tabbatar da cewa ikirarin da ake yadawa ba gaskiya bane domin kuwa taron da ake magana bai sami sahalewar gwamnatin Saudiyya ba, haka zalika gwamnatin Najeriya bazata shiga ko aike da kowa zuwa taron ba domin tana zargin ‘yan damfara ne suka shirya. Don haka wannan ikirari ya zama karya wato false a turance.