A ƙarshe-ƙarshen shekarar 2025 ne dai aka fara samun hare-haren yan fashin daji a wasu yankunan arewacin Kano.
Iƙirari:
Tun ranar Litinin 2 ga watan Fabrairun 2026, ake ta yaɗa jita-jita a shafukan sada zumunta da kuma gari cewa an ga wani makiyayi a kasuwar saida kayan abinci ta Dawanau ta jihar Kano ɗauke da bindiga a rataye yana tafiya da dabbobi. Wani shafin Facebook mai suna Adamu MB ya wallafa wani bidiyo dake wannan ikirari.
Wani shafin ma mai suna DOVE NEWS HAUSA shima ya wallafa wannan labari.
Wannan labarin ya haifar da firgici da rudani a tsakanin jama’a, inda aka ɗauka cewa masu garkuwa da mutane ne ko ‘yan bindiga ne suka shigo yankin.
Bincike:
Kafar tantance labarai ta Alkalanci ta gudanar da bincike na musamman don gano gaskiyar lamarin ta hanyar tuntuɓar hukuma da kuma duba sahihan majiyoyi.
Mun tuntuɓi daya daga cikin jami’an tsaro da ke aiki a ɗaya daga ofisoshin ‘yan sanda da ke jahar inda ya tabbatar mana ba shi da wannan labari ma gaba ɗaya. Sannan mun duba shafukan sada zumunta na hukumar ‘yan sanda, nan ma ba a wallafa wannan labari ba sannan babu wani sahihin gidan jarida kamar BBC ko Daily Trust da suka wallafa labarin.
A al’ada, idan irin wannan babban al’amari na tsaro ya faru a babbar kasuwa irin ta Dawanau, hukumomin tsaro sukan fitar da sanarwa ko kuma manyan jaridu su ɗauki rahoto, amma babu ko ɗaya daga ciki da ya tabbatar da hakan.
Sai dai binciken ya tabbatar da cewa wanda aka gani dauke da bindiga jami’in tsaro ne dake raka dabbobin da jami’an tsaro suka kwato.
Sakamakon Bincike:
Bisa la’akari da rashin samun hujja daga hukumar ‘yan sanda da kuma rashin ganin labarin a sahihan kafafen yaɗa labarai, Alkalanci ta tabbatar da cewa wannan labari ƙarya ne.
