BindiddigiIna gaskiyar ganawar Tinubu da Kwankwaso?

Ina gaskiyar ganawar Tinubu da Kwankwaso?

-

Hukunci: Ƙarya ne
Bisa kasa samun bidiyo da hotuna daga shafukan fadar shugaban kasa, da kuma tabbacin cewa bidiyo da hotunan tsoffi ne wadanda aka dauka a shekarar 2023 yasa Alkalanci cewa kokarin kawar da hankali ne.
Ikirari:
Wani shafin Facebook mai suna Tijjani Tj Hamza ya wallafa wani bidiyo inda yayi ikirarin cewa;
“Kwankwaso ya gana da shugaban kasa Bola Ahmed Tunubu, sun tattauna batun ceto Nigeria da kuma batun siyasa.”
Hoton tsohon bidiyo da ke cigaba da yaduwa
Shima wani shafin mai suna Yahuza Abdullahi ya wallafa irin wancan bidiyo ((https://www.facebook.com/share/r/15zd5YUEyM/?))
Tsohon hoto da ke cigaba da yaduwa
Wani shafin na Facebook shi kuma ya wallafa hotuna tare da ikirari cewa Kwankwaso ya gana da
“Kwankwaso ya gana da shugaban kasa Bola Tinubu a shirye shiryensa ba komawa jamiyyar APC“
Tsoffin hotuna da ke cigaba da yaduwa
Bincike:
Kafar tantance labarai ta Alkalanci ta duba shafin mai magana da yawun shugaban Najeriya inda babu wata wallafa makamanciyar wannan, haka zalika babu wannan bidiyo ko hotuna a shafin Sanata Kwankwaso.
Alkalanci ta gano cewa bidiyon da ake wallafawa tare da ikirarin cewa Sanata Kwankwaso ya gana da shugaba Tinubu tsohon bidiyo ne da aka dauka a watan Yunin shekarar 2023. Kamar yadda yake a wannan bidiyo da gidan jaridar TVC ya wallafa a wancan shekarar ta 2023.
Su ma hotunan an dauke su ne a shekarar ta 2023 kamar yadda gidan jaridar BBC Hausa ta wallafa a waccen shekarar.
Sakamakon bincike:
Bisa kasa samun bidiyo da hotuna daga fadar shugaban kasa da shafin Sanata Kwankwaso, da kuma samun tabbacin cewa bidiyo da hotunan da ake yadawa an dauke su ne a shekarar 2023 yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa kokarin kawar da hankulan mutane ne.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Shin an nemi wulakanta Shugaban Burkina Faso a Faransa?

A cikin ‘yan shekarun nan an cigaba da samun labaran karya musamman dake da alaka da kasar Burkina Faso. Ikirari: Wani...

Shin da gaske akwai ‘yar tsama tsakanin Tinubu da Kashim?

Tun bayan dawowar damakradiyya a shekarar 1999 za’a iya cewa samun rashin jituwa tsakanin shugaban kasa da mataimakinsa ba...

Waɗanne ƙasashe ake ganin suna goyon bayan kafa gwamnatin ƴan tawaye a Sudan?

Ayyana gwamnatin ƴan tawaye da jagoran RSF Laftanar-Janar Mohamed Hamdan Dagalo ya yi a Sudan, ya zo a daidai lokacin...

Mutum uku ne suka mutu a hadarin hanyar Abuja zuwa Lokoja ba sama da mutane 100 ba

  Ikirari: Wani shafin Facebook mai suna Karaduwa post ya wallafa wani labari tare da hotuna wanda ya yadu matuka da...

CBEX: Yadda zaku gane Idan kamfanin sanya hannun jari na da rijista

A ‘yan kwanakin nan an ga wasu rahotanni da suka bayyana cewa ‘yan Najeriya sunyi asarar makudan kudade yayin...

Cirani: Shin Tarayyar Turai ta amince ‘yan Afrika su tsallaka ta Libya ba tare da Biza ba?

Duk da cewa kasashen turai na nuna damuwa tare da daukar matakan rage shigar bakin haure, ‘yan cirani dake...

Karanta wannan

Shin an nemi wulakanta Shugaban Burkina Faso a Faransa?

A cikin ‘yan shekarun nan an cigaba da samun...

Shin da gaske akwai ‘yar tsama tsakanin Tinubu da Kashim?

Tun bayan dawowar damakradiyya a shekarar 1999 za’a iya...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar