Fayyace abubuwaƙasar Jamhuriyar Czech ta sanya batun matsalolin labaran ƙarya...

ƙasar Jamhuriyar Czech ta sanya batun matsalolin labaran ƙarya cikin taron tsaro na duniya

-

 

A ranakun 12 zuwa 14 ga watan Yuni ne dai ƙasar jamhuriyyar Czech ta karɓi baƙuncin shugabannin wasu ƙasashe, kwararru a fannonin tsaro, jarida da wasu fannoni da dama a taron ƙasa da ƙasa kan tsaro a faɗin duniya.

               Shugaban kasar Czhechia Petr Pavel

Taron wanda shugaban ƙasar Ukraine Vladimir Zelensky ya yi jawabi kan cewa Rasha ba zata daina kai hare-hare kan Ukraine ba sai ƙasashen duniya sun matsa wa shugaban Rasha Vladimir Putin lamba.
Ya ƙara da cewa idan har ƙasashen duniya suka bari Rasha ta sami nasarar mamaye Ukraine tare da fara mulkin mallakar da take son yi to fa Babu tabbacin wacce ƙasace ta gaba a gabashin Turai.
A nasa jawabin shugaban kasar Czech Petr Pavel ya bayyana muhimmancin taron tsaro musamman ta samar da sashen tattaunawa kan batutuwa masu matuƙar muhimmanci.
Taron ya ƙara da jaddada goyon baya da kuma tabbatar da bada goyon baya ga ƙasashen gabashin Turai.

Batun matsalolin labaran ƙarya
A taron an tattauna kan barazanar labaran ƙarya da kuma amfani da ƙirƙirrarriyar basirar AI wajen Farfaganda da sauya tunanin matane a ƙasashen Turai da wasu ƙasashen Afrika.
Taron dai ya jaddada buƙatar ƙasashen Tarayyar Turai EU su maida hankali kan wayar da kan mutane kan ilimin samun sahihan labarai wato media literacy. An bayyana ƙasashen Slovakia, France da Jamus na kan gaba wajen barazanar matsalolin labaran karya daga ƙasar waje wato FIMI.
Haka zalika an bayyana hotuna da bidiyo da ake amfani da ƙirƙirrarriyar basirar AI wajen haddasa rikici da bata sunayen ƙasashe da dama.
Editan Alkalanci Alhassan Bala ya sami damar halartar taron tsaron na ƙasa da ƙasa GlobalSec 2025 a birnin Prague inda ya halarci zama kan batun labaran ƙarya da kuma batun matasa, matsalar tsaro da kuma ruwan sha.

Editan Alkalanci Alhassan Bala a taron tsaro na duniya a birnin Prague

Bala na cikin ƴan jaridun Afrika 11 da ƙasar ta Czechia ta gayyata don su halarci taron. Yayin taron ya gana da masu ruwa da tsaki kan harkokin yaƙi da labaran ƙarya daga sassan duniya.
Ya bayyana farin cikin sa na ganin cewa an gano tare da amincewa da barazanar labaran ƙarya ga zaman lafiyar duniya.
Har ila yau Editan na Alkalanci ya sami tattaunawa da shugaba ƙasar ta Czechia Petr Pavel inda ya jaddada goyon bayan yaƙi da labaran da kuma kawo harkokin cigaba a ƙasashen Afrika.

Tattaunawar yan jaridun Afrika da Shugaban kasar Czhechia
Editan Alkalanci tare da shugaban Czhech Petr Pavel

Ƙasar jamhuriyyar Czech dai na cikin ƙasashen Turai da basu taɓa yiwa kowacce kasar Afrika mulkin mallaka ba.
Kuma tana cikin ƙasashen tsakiya da gabashin Turai da suka sha baƙar wuya daga hannun Turawan ƙasar Jamus da kuma mulkin mallaka da kisa daga Rasha.

Tattaunawa da jagororin ma’aikatar harkokin wajen Czhech

Yayin wata ganawa da ƴan jaridun daga ƙasashen Afrika 8, jagororin ma’aikatar harkokin wajen ƙasar Czech sun jaddada cewa akwai buƙatar ƙasashen Afrika su bi a hankali wajen alaƙa da ƙasar Rasha domin Czech na cikin ƙasashen da suka ɗanɗana kuɗarsu a hannun Rasha a shekarun baya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Ina gaskiyar labari da hotunan baiwa ƴan wasan Super Eagles gidaje da motoci

Bayan da aka kammala gasar cin kofin Nahiyar Afirka AFCON wanda Najeriya ta zo ta biyu, akwai labarai kala-kala...

Bidiyon da ake yaɗawa ba na waɗanda sukai kisan Ɗorayi bane 

Ƴan Najeriya dai na cigaba da jimami tare da Allah wadai da kisan wasu ƴan gida ɗaya su bakwai...

Hotunan samuwar makaman kariya zuwa Burkina Faso daga Rasha da China hadin AI ne

  Yayin da Rasha da ƙasar Sin ke ci gaba da tura makamai zuwa yankin Sahel, wani hoto da bidiyo...

Labarin cewa Aisha Buhari ta amince ta auri Sheikh Isa Ali Pantami ƙarya ne

Tun bayan kammala iddar tsohuwar matar shugaban kasa Muhammadu Buhari ake ta yada wasu labarai da iƙirarai kala-kala wanda...

Gwamna Abba Kabir Yusuf bai cire Mustapha Kwankwaso daga muƙaminsa ba

A ƙarshen watan Disemba ne dadi aka sami labarin cewa gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf zai sauya sheƙa...

Me yasa Amurka ta kai hari Sokoto?

Kasar Amurka ta takaddamar da hare-hare a wasu yankuna a arewacin Najeriya. Yanku nan sun hada da Arewa maso...

Karanta wannan

Ina gaskiyar labari da hotunan baiwa ƴan wasan Super Eagles gidaje da motoci

Bayan da aka kammala gasar cin kofin Nahiyar Afirka...

Bidiyon da ake yaɗawa ba na waɗanda sukai kisan Ɗorayi bane 

Ƴan Najeriya dai na cigaba da jimami tare da...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar