Fayyace abubuwaƙasar Jamhuriyar Czech ta sanya batun matsalolin labaran ƙarya...

ƙasar Jamhuriyar Czech ta sanya batun matsalolin labaran ƙarya cikin taron tsaro na duniya

-

 

A ranakun 12 zuwa 14 ga watan Yuni ne dai ƙasar jamhuriyyar Czech ta karɓi baƙuncin shugabannin wasu ƙasashe, kwararru a fannonin tsaro, jarida da wasu fannoni da dama a taron ƙasa da ƙasa kan tsaro a faɗin duniya.

               Shugaban kasar Czhechia Petr Pavel

Taron wanda shugaban ƙasar Ukraine Vladimir Zelensky ya yi jawabi kan cewa Rasha ba zata daina kai hare-hare kan Ukraine ba sai ƙasashen duniya sun matsa wa shugaban Rasha Vladimir Putin lamba.
Ya ƙara da cewa idan har ƙasashen duniya suka bari Rasha ta sami nasarar mamaye Ukraine tare da fara mulkin mallakar da take son yi to fa Babu tabbacin wacce ƙasace ta gaba a gabashin Turai.
A nasa jawabin shugaban kasar Czech Petr Pavel ya bayyana muhimmancin taron tsaro musamman ta samar da sashen tattaunawa kan batutuwa masu matuƙar muhimmanci.
Taron ya ƙara da jaddada goyon baya da kuma tabbatar da bada goyon baya ga ƙasashen gabashin Turai.

Batun matsalolin labaran ƙarya
A taron an tattauna kan barazanar labaran ƙarya da kuma amfani da ƙirƙirrarriyar basirar AI wajen Farfaganda da sauya tunanin matane a ƙasashen Turai da wasu ƙasashen Afrika.
Taron dai ya jaddada buƙatar ƙasashen Tarayyar Turai EU su maida hankali kan wayar da kan mutane kan ilimin samun sahihan labarai wato media literacy. An bayyana ƙasashen Slovakia, France da Jamus na kan gaba wajen barazanar matsalolin labaran karya daga ƙasar waje wato FIMI.
Haka zalika an bayyana hotuna da bidiyo da ake amfani da ƙirƙirrarriyar basirar AI wajen haddasa rikici da bata sunayen ƙasashe da dama.
Editan Alkalanci Alhassan Bala ya sami damar halartar taron tsaron na ƙasa da ƙasa GlobalSec 2025 a birnin Prague inda ya halarci zama kan batun labaran ƙarya da kuma batun matasa, matsalar tsaro da kuma ruwan sha.

Editan Alkalanci Alhassan Bala a taron tsaro na duniya a birnin Prague

Bala na cikin ƴan jaridun Afrika 11 da ƙasar ta Czechia ta gayyata don su halarci taron. Yayin taron ya gana da masu ruwa da tsaki kan harkokin yaƙi da labaran ƙarya daga sassan duniya.
Ya bayyana farin cikin sa na ganin cewa an gano tare da amincewa da barazanar labaran ƙarya ga zaman lafiyar duniya.
Har ila yau Editan na Alkalanci ya sami tattaunawa da shugaba ƙasar ta Czechia Petr Pavel inda ya jaddada goyon bayan yaƙi da labaran da kuma kawo harkokin cigaba a ƙasashen Afrika.

Tattaunawar yan jaridun Afrika da Shugaban kasar Czhechia
Editan Alkalanci tare da shugaban Czhech Petr Pavel

Ƙasar jamhuriyyar Czech dai na cikin ƙasashen Turai da basu taɓa yiwa kowacce kasar Afrika mulkin mallaka ba.
Kuma tana cikin ƙasashen tsakiya da gabashin Turai da suka sha baƙar wuya daga hannun Turawan ƙasar Jamus da kuma mulkin mallaka da kisa daga Rasha.

Tattaunawa da jagororin ma’aikatar harkokin wajen Czhech

Yayin wata ganawa da ƴan jaridun daga ƙasashen Afrika 8, jagororin ma’aikatar harkokin wajen ƙasar Czech sun jaddada cewa akwai buƙatar ƙasashen Afrika su bi a hankali wajen alaƙa da ƙasar Rasha domin Czech na cikin ƙasashen da suka ɗanɗana kuɗarsu a hannun Rasha a shekarun baya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya da suka shafi bangarorin biyu wato bangaren Sarki Aminu Ado...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan kiyashin kiristoci a Najeriya da kuma bayanin yiwuwar turo da...

Bidiyon Nnamdi Kanu a gidan yarin Sokoto haɗin AI ne 

Bayan hukuncin da koto tayi na ɗaure Nnamdi Kanu bisa laifin ta'addanci, hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta...

Rasha da Amurka ne kan gaba wajen yaɗa labaran ƙarya a yammacin Afirka cewar Fauziyya Kabir Tukur

Shekara da shekaru ƙasashen duniya kanyi amfani da yaɗa labarai wajen yaƙi da juna ko haddasa rikici a wasu...

ƙirƙirarrayir basirar AI wanne hali Najeriya ke ciki?

A cikin watan Satumba, 2025 aka samu wani shafi na caca ya ƙirƙiri bidiyo da hoton talla na ƙarya...

Ƙarya ne: Saudiyya bata cire ɗarikar Tijjaniyya daga cikin akidu da ke da alaka da musulunci ba

Wani shafin TikTok mai suna prince hassan ya wallafa labarin cewa hukumar Saudiyya ta cire Tijjaniyya cikin jerin akidun...

Karanta wannan

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar