BindiddigiƘarya ne: Ba a kwantar da Dr. Zakir Naik...

Ƙarya ne: Ba a kwantar da Dr. Zakir Naik a asibiti ba

-

Hukunci: Ƙarya ne
Bisa samun sahihin gidan jarida a ƙasar Malasiya mai suna Free Malaysia Today FMT daya zanta da lauyan Dr. Zakir Naik mai suna Akbedin Abdul Kadir wanda ya ƙaryata labarin. Sannan Alkalanci ta ka sa samun wata sahihiyar kafar sadarwa ko jarida data wallafa labarin. Bugu da ƙari ganin cewa Dr. Zakir Naik ya cigaba da wallafa bayanai a shafin sa na X, yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa labarin ƙarya ne.
Akwai labarai dake yaɗuwa a kafafen sada zumunta dake iƙirarin cewa shahararren mai wa’azi da da’awa dan ƙasar Indiya Dr. Zakir Naik na kwance a asibiti bashi lafiya a ƙasar Malaysia.
Iƙirarin:
Wani shafin Facebook mai suna Vanguard Hausa ya wallafa wannan labari a daren ranar 10 ga watan Satumbar 2025. Shafin ya rubuta labarin kamar haka;
YANZU-YANZU: Rahotanni Na Cewa Ankwantar Da Fitaccen Malamin Addinin musulunci Sheikh Zakir Naik A Wani Asibiti A Kasar Malesiya Cikin Mawuyacin Hali
Al’ummar musulmai Ku tayashi da Addu’a
Ku Turawa Yan uwa SU sanyashi acikin Addu’a.” 
Cikin awanni 17 wallafar ta sami tofa albarkacin baki wato comments sama da dubu goma sha ɗaya, sannan sama da mutum dubu biyu sukai sharing.
Labarin ƙarya dake cigaba da yaduwa

((https://www.facebook.com/share/p/1B9ve1kRdA/?mibextid=wwXIfr))

Haka zalika wani shafi mai suna A T V Hausa shima ya wallafa labarin a ranar 11 ga watan Satumbar 2025 inda alamu suka nuna ya kwafa ne kai tsaye daga Vanguard Hausa. Mutane sama da dubu ɗaya da ɗari biyar ne suka tofa albarkacin baki wato comments, yayin da sama da mutane dayri biyu da casa’in sukai sharing cikin awanni 7 da wallafa wa.
Labarin karya dake cigaba da yaduwa
Bincike:
Kafar tantance labarai ta Alkalanci ta duba tare da bincika sahihan gidajen jaridu a ƙasar Malasiya da India amma babu wacce ta tabbatar da wannan labarai.
Kafafen labaran Indiya
Ƙasar Indiya dai na neman Dr. Zakir ruwa a jallo bisa zarge-zarge da dama da suka haɗa da ta’addanci. Wasu kafafen jaridun Indiya sun rawaito yadda ake yaɗa jita-jitar cewa ya kamu da cutar HIV yana asibiti. Amma sun tabbatar babu wani tabbacin labarin, sun ƙara da cewa babu wata sahihiyar kafar yada labarai data rawaito labarin.
Kafafen labaran Malasiya 
To sai dai kafar yada labarai a kasar Malasiya mai suna Free Malaysia Today FMT ta rawaito cewa labarin ƙarya ne.
Domin kuwa Lauyan Shaikh Zakir Naik mai suna Akbedin Abdul Kadir musanta labarin tare da cewa zugi ta malle ce kawai.

Labarin da gidan jaridar FMT ta rawaito na karya cewa an kwantar da Dr. Zakir Naik

((https://www.freemalaysiatoday.com/category/nation/2025/09/09/i-dont-have-aids-says-zakir-naik)

Haka zalika Alkalanci ta duba shafin X (Twitter) din Dr. Zakir Naik inda ta ga cewa ya cigaba da wallafa abubuwa a shafin sa kamar yadda ya saba.
Hoton shafin X din Dr. Zakir Naik an wallafa abubuwa
Sakamakon bincike:
Bisa samun sahihin gidan jarida a ƙasar Malasiya mai suna Free Malaysia Today FMT daya zanta  da lauyan Dr. Zakir Naik mai suna Akbedin Abdul Kadir wanda ya ƙaryata labarin. Sannan Alkalanci ta ka sa samun wata sahihiyar kafar sadarwa ko jarida data wallafa labarin. Bugu da ƙari ganin cewa Dr. Zakir Naik ya cigaba da wallafa bayanai a shafin sa na X, yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa labarin ƙarya ne.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Ina gaskiyar Iƙirarin mai da waɗanda ake zargi da kisa a Kano zuwa kudancin Najeriya?

IƙirariWani bidiyo yana ta yaɗuwa a kafar sada zumunta ta TikTok wanda ke nuna cewa jami'an tsaro sun kwashe...

Ina gaskiyar labari da hotunan baiwa ƴan wasan Super Eagles gidaje da motoci

Bayan da aka kammala gasar cin kofin Nahiyar Afirka AFCON wanda Najeriya ta zo ta biyu, akwai labarai kala-kala...

Bidiyon da ake yaɗawa ba na waɗanda sukai kisan Ɗorayi bane 

Ƴan Najeriya dai na cigaba da jimami tare da Allah wadai da kisan wasu ƴan gida ɗaya su bakwai...

Hotunan samuwar makaman kariya zuwa Burkina Faso daga Rasha da China hadin AI ne

  Yayin da Rasha da ƙasar Sin ke ci gaba da tura makamai zuwa yankin Sahel, wani hoto da bidiyo...

Labarin cewa Aisha Buhari ta amince ta auri Sheikh Isa Ali Pantami ƙarya ne

Tun bayan kammala iddar tsohuwar matar shugaban kasa Muhammadu Buhari ake ta yada wasu labarai da iƙirarai kala-kala wanda...

Gwamna Abba Kabir Yusuf bai cire Mustapha Kwankwaso daga muƙaminsa ba

A ƙarshen watan Disemba ne dadi aka sami labarin cewa gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf zai sauya sheƙa...

Karanta wannan

Ina gaskiyar Iƙirarin mai da waɗanda ake zargi da kisa a Kano zuwa kudancin Najeriya?

IƙirariWani bidiyo yana ta yaɗuwa a kafar sada zumunta...

Ina gaskiyar labari da hotunan baiwa ƴan wasan Super Eagles gidaje da motoci

Bayan da aka kammala gasar cin kofin Nahiyar Afirka...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar