BindiddigiƘarya ne: Ba a kwantar da Dr. Zakir Naik...

Ƙarya ne: Ba a kwantar da Dr. Zakir Naik a asibiti ba

-

Hukunci: Ƙarya ne
Bisa samun sahihin gidan jarida a ƙasar Malasiya mai suna Free Malaysia Today FMT daya zanta da lauyan Dr. Zakir Naik mai suna Akbedin Abdul Kadir wanda ya ƙaryata labarin. Sannan Alkalanci ta ka sa samun wata sahihiyar kafar sadarwa ko jarida data wallafa labarin. Bugu da ƙari ganin cewa Dr. Zakir Naik ya cigaba da wallafa bayanai a shafin sa na X, yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa labarin ƙarya ne.
Akwai labarai dake yaɗuwa a kafafen sada zumunta dake iƙirarin cewa shahararren mai wa’azi da da’awa dan ƙasar Indiya Dr. Zakir Naik na kwance a asibiti bashi lafiya a ƙasar Malaysia.
Iƙirarin:
Wani shafin Facebook mai suna Vanguard Hausa ya wallafa wannan labari a daren ranar 10 ga watan Satumbar 2025. Shafin ya rubuta labarin kamar haka;
YANZU-YANZU: Rahotanni Na Cewa Ankwantar Da Fitaccen Malamin Addinin musulunci Sheikh Zakir Naik A Wani Asibiti A Kasar Malesiya Cikin Mawuyacin Hali
Al’ummar musulmai Ku tayashi da Addu’a
Ku Turawa Yan uwa SU sanyashi acikin Addu’a.” 
Cikin awanni 17 wallafar ta sami tofa albarkacin baki wato comments sama da dubu goma sha ɗaya, sannan sama da mutum dubu biyu sukai sharing.
Labarin ƙarya dake cigaba da yaduwa

((https://www.facebook.com/share/p/1B9ve1kRdA/?mibextid=wwXIfr))

Haka zalika wani shafi mai suna A T V Hausa shima ya wallafa labarin a ranar 11 ga watan Satumbar 2025 inda alamu suka nuna ya kwafa ne kai tsaye daga Vanguard Hausa. Mutane sama da dubu ɗaya da ɗari biyar ne suka tofa albarkacin baki wato comments, yayin da sama da mutane dayri biyu da casa’in sukai sharing cikin awanni 7 da wallafa wa.
Labarin karya dake cigaba da yaduwa
Bincike:
Kafar tantance labarai ta Alkalanci ta duba tare da bincika sahihan gidajen jaridu a ƙasar Malasiya da India amma babu wacce ta tabbatar da wannan labarai.
Kafafen labaran Indiya
Ƙasar Indiya dai na neman Dr. Zakir ruwa a jallo bisa zarge-zarge da dama da suka haɗa da ta’addanci. Wasu kafafen jaridun Indiya sun rawaito yadda ake yaɗa jita-jitar cewa ya kamu da cutar HIV yana asibiti. Amma sun tabbatar babu wani tabbacin labarin, sun ƙara da cewa babu wata sahihiyar kafar yada labarai data rawaito labarin.
Kafafen labaran Malasiya 
To sai dai kafar yada labarai a kasar Malasiya mai suna Free Malaysia Today FMT ta rawaito cewa labarin ƙarya ne.
Domin kuwa Lauyan Shaikh Zakir Naik mai suna Akbedin Abdul Kadir musanta labarin tare da cewa zugi ta malle ce kawai.

Labarin da gidan jaridar FMT ta rawaito na karya cewa an kwantar da Dr. Zakir Naik

((https://www.freemalaysiatoday.com/category/nation/2025/09/09/i-dont-have-aids-says-zakir-naik)

Haka zalika Alkalanci ta duba shafin X (Twitter) din Dr. Zakir Naik inda ta ga cewa ya cigaba da wallafa abubuwa a shafin sa kamar yadda ya saba.
Hoton shafin X din Dr. Zakir Naik an wallafa abubuwa
Sakamakon bincike:
Bisa samun sahihin gidan jarida a ƙasar Malasiya mai suna Free Malaysia Today FMT daya zanta  da lauyan Dr. Zakir Naik mai suna Akbedin Abdul Kadir wanda ya ƙaryata labarin. Sannan Alkalanci ta ka sa samun wata sahihiyar kafar sadarwa ko jarida data wallafa labarin. Bugu da ƙari ganin cewa Dr. Zakir Naik ya cigaba da wallafa bayanai a shafin sa na X, yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa labarin ƙarya ne.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya da suka shafi bangarorin biyu wato bangaren Sarki Aminu Ado...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan kiyashin kiristoci a Najeriya da kuma bayanin yiwuwar turo da...

Bidiyon Nnamdi Kanu a gidan yarin Sokoto haɗin AI ne 

Bayan hukuncin da koto tayi na ɗaure Nnamdi Kanu bisa laifin ta'addanci, hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta...

Rasha da Amurka ne kan gaba wajen yaɗa labaran ƙarya a yammacin Afirka cewar Fauziyya Kabir Tukur

Shekara da shekaru ƙasashen duniya kanyi amfani da yaɗa labarai wajen yaƙi da juna ko haddasa rikici a wasu...

ƙirƙirarrayir basirar AI wanne hali Najeriya ke ciki?

A cikin watan Satumba, 2025 aka samu wani shafi na caca ya ƙirƙiri bidiyo da hoton talla na ƙarya...

Ƙarya ne: Saudiyya bata cire ɗarikar Tijjaniyya daga cikin akidu da ke da alaka da musulunci ba

Wani shafin TikTok mai suna prince hassan ya wallafa labarin cewa hukumar Saudiyya ta cire Tijjaniyya cikin jerin akidun...

Karanta wannan

Labarin cewa Christopher Musa ya bai wa Aminu Ado Bayero wa’adin awa 24 ya je ya same shi, ƙarya ne

Tun bayan tababar sarautar Kano ake samun labaran karya...

Labaran ƙarya da ake yadawa kan kalaman Trump a shafukan Facebook

Tun bayan iƙirarin shugaban Amurka Donald Trump na kisan...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar