Hukunci: Ƙarya ne
Wannan wani sanannen labarin ƙarya ne da ake ta faman maimaita yaɗa shi a shafukan sada zumunta na Facebook. Masu bincike suna ayyana irin wannan labari a matsayin "Zombie Story”, wato labarin da aka riga aka tabbatar da ƙaryarsa amma yake sake tashi lokaci bayan lokaci.
“Shugaban Rasha Putin ya saka dokar hukunci mai tsanani ga duk mutumin da aka kama shi yana ɓatanci ga Manzon Allah (SAW), ko kuma ya ƙona Alkur’ani mai girma.”
Wannan wani sanannen labarin ƙarya ne da ake ta faman maimaita yaɗa shi a shafukan sada zumunta na Facebook. Masu bincike suna ayyana irin wannan labari a matsayin “Zombie Story”, wato labarin da aka riga aka tabbatar da ƙaryarsa amma yake sake tashi lokaci bayan lokaci.
Asalin Labarin
Tushen wannan labari ya samo asali ne daga ziyarar da shugaban ƙasar Rasha,
Vladimir Putin, ya kai babban masallacin Juma’a na birnin Derbent ranar 28 ga watan Yuni, 2023 (lokacin bikin Sallar Layya). Manufar ziyarar ita ce duba wuraren tarihi don bunƙasa harkokin yawon buɗe ido.
A yayin wannan ziyara, an bai wa Putin kyautar Alkur’ani, inda ya bayyana cewa a ƙasar Rasha, mutunta Alkur’ani wajibi ne, kuma ƙona shi babban laifi ne a ƙarƙashin kundin tsarin mulkin ƙasar da kuma dokar hukunta manyan laifuka (Article 282). Sai dai, Putin bai sanya wata sabuwar doka ba a lokacin; yana magana ne kan tsohuwar dokar da ake da ita.
Yadda aka Sauya Labarin
Bayan wannan ziyara, wasu shafukan watsa labarai da na sada zumunta suka fara juya maganar shugaban, suna iƙirarin cewa ya “sanya sabuwar doka” ko ma “hukuncin mai tsanani” ga masu ɓatanci.
• Shafin ofishin
jakadancin Rasha da ke Karachi ya fitar da bayani ranar 3 ga watan Yuli, 2023, game da matsayin Rasha kan ƙona Alkur’ani a Sweden, wanda wasu suka yi amfani da shi wajen ƙirƙirar nasu labarin na ƙarya.
• Shafin gidan jarida na
TRT World ma ya wallafa bidiyon kalaman Putin ranar 29 ga watan Yuni, 2023, inda shugaban ke cewa ƙona Alkur’ani laifi ne a Rasha, amma ba wai an yi sabuwar doka ba ne.
Sake Maimaituwar Labarin
Duk da cewa wannan abu ya faru tun a 2023, wasu shafukan na Hausa sai suka ci gaba da yaɗa shi a matsayin sabon labari a farkon shekarar 2025 da ƙarshenta. Kuma suka nuna ai a shekarar ne ta 2025 abin ya faru. Ga wasu daga cikin labaran:
• Shafin ATV Hausa: Ya sake wallafa labarin a
watan Nuwamba, 2025, sannan ya sake
maimaitawa a watan Disamba, 2025.
• Shafin Diffa Studio TV: Ya sake yaɗa
wannan labari a watan Oktoba, 2025.
Wannan na nuna yadda shafukan sada zumunta ke amfani da labaran da suka shafi addini don samun mabiya ta hanyar yaɗa tsohon labari a matsayin sabo ko kuma su canza labarin gabaɗaya daga yadda yake a asali, wanda hakan wata hanya ce ta yaudarar jama’a.