Yayin da ake cigaba da takaddama kan batun ko duk wanda za a baiwa mukamin minista sai ya kasance yana da rijista da jam’iyyar siyasa, lauya Deji Adeyanju ya yiwa Alkalanci karin bayani kan wannan batu.
Idan ana buƙatar yiwa wannan batun cewa duk wanda zai rike ko za a naɗa muƙamin minista a Najeriya sai ya kasance yana da rijista da wata jam’iyya siyasa to sai an duba kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999 da akawa kwaskwarima.
Me sashe 147(5) ya ce?
Wannan sashe na 147 (5) ya ce duk wanda za a naɗa muƙamin minista a Najeriya dole sai ya cika sharuɗɗan a zaɓe shi a matsayin ɗan majalisar wakilai. To amma wannan sashe ba tilo bane domin ya bayyana sashe 65(2) (b) inda yace mutum zai cancanta a zaɓe shi ɗan majalisar wakilai idan yana da jam’iyyar siyasa kuma jam’iyyar siyasa ta ɗauki nauyin sa. Wannan na iya fassaruwa matsayin duk wanda za a naɗa muƙamin minista sai yana da jam’iyyar siyasa.
To amma kundin tsarin mulkin ya ƙara da cewa ba dole sai wanda za a naɗa ministan ya kasance ɗan jam’iyyar da shugaban ƙasa ya fito ba wato ba sai ƴan jam’iyya mai ci ba kaɗai.
Da zarar an sami cikar waɗannan sharuɗɗa sashe na 141(1) ya baiwa shugaban ƙasa dama ya naɗa minista bayan sahalewar majalisar dattawa.
To amma batun dole ka zama ɗan jam’iyyar shugaban ƙasa to babu inda kundin tsarin mulkin Najeriya ya ce haka.
Wannan yasa zaka iya ganin minista ya fito daga
