BindiddigiLabarin karya kan shugaban Faransa dangane da Burkina Faso

Labarin karya kan shugaban Faransa dangane da Burkina Faso

-

Hukunci: Ƙarya ne
Binciken Alkalanci ta hanyar tuntubar ma’aikatar harkokin wajen Burkina Faso inda suka ce basu da masaniyar wannan labari. Sannan kasa samun wata sahihiyar kafar labarai data rawaito wannan labari ya sa Alkalanci yanke hukuncin cewa labarin karya ne.
Takun sakar dake tsakanin shugaban kasar Burkina Faso da kasar Faransa ba abu ne boyayye ba.
Akwai dai zarge-zarge da dama kan kasar Faransa da ayyukan ta a wasu kasashen data raina wanda ya hada da Burkina Faso.
Akwai dai kalaman shugaban kasar na Faransa da yayi a kwanakin baya na cewa ya kamata kasashen da suka raina su godewa Faransa amma sai gashi sun sami akasin haka. Wadannan kalamai sun jawo cecekuce daga shugabannin kasashen da Faransa ta raina.
Tun bayan wannan jawabi ne dai ake samun labaran karya da ake alakantawa da shugaban Faransa ko kasar ta Faransa.
Wani shafin Facebook mai suna Hausawa (https://www.facebook.com/share/p/16eaav7KWa/?) ya wallafa wani labari dake cewa; Shugaban Faransa Macron ya sha alwashin ganin ya kubutar da Mutanen Burkina Faso daga hannun shugaba Ibrahim Traoré.
Hoton labarin karya dake cigaba da yaduwa
Shi ma ya wallafa wannan ikirari.
Bincike:
Kasar Faransa dai ta kwashe dukkan sojojin ta daga kasashen Burkina Faso, Niger, Mali, Chad bayan da kasashen suka bukaci hakan.
Wannan sabon labarin dai ya fito ne daga shafin X din @LegitTargets wanda shafi ne kafafen tantance labarai da dama suka tantance labaran da shafin ke yadawa tare da samun shafin da yada labaran karya sosai.
Binciken Alkalanci bai samo wannan labari a kowanne irin sahihin shafin labarai ba na turanci ko na Faransanci.
Wani jami’in ma’aikatar harkokin wajen Faransa ya bayyanawa Alkalanci cewa wannan labarin karya ne, domin babu wani abu makamancin haka da shugaba Macron ya fada.
Ma’aikatar ta kara da cewa wannan labari wani salo ne na masu yada labaran karya da bata sunan kasar Faransa a idanun mutane.
Alkalanci ta tuntubi wani jami’in ma’aikatar harkokin wajen Burkina Faso inda jami’in yace basu ga wannan labari ba. Ya ce tabbas ‘yan Burkina Faso sunyi murnar barin Faransa kasarsu amma bai san da wancan labarin ba.
Sakamakon bincike:
Kasancewar ba a sami wata sahihiyar kafar labarai data rawaito wannan labari ba, sannan musanta labarin da ma’aikatar harkokin wajen Faransa tayi da kuma ta kasar Burkina Faso da tace bata da masaniyar wannan labari, wannan yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa wannan labari karya ne.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Aisha Buhari ta amince ta auri Sheikh Isa Ali Pantami ƙarya ne

Tun bayan kammala iddar tsohuwar matar shugaban kasa Muhammadu Buhari ake ta yada wasu labarai da iƙirarai kala-kala wanda...

Gwamna Abba Kabir Yusuf bai cire Mustapha Kwankwaso daga muƙaminsa ba

A ƙarshen watan Disemba ne dadi aka sami labarin cewa gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf zai sauya sheƙa...

Me yasa Amurka ta kai hari Sokoto?

Kasar Amurka ta takaddamar da hare-hare a wasu yankuna a arewacin Najeriya. Yanku nan sun hada da Arewa maso...

Duk da Iƙirarin gwamnatin Katsina Ameena Dikko Radda na da shafin Instagram tun 2018

Akwai wani hoto daya yaɗu matuƙa game da yar gwamnan jahar Katsina mai suna Amina dikko Radda inda aka...

Abunda ya kamata ku sani dangane da makamin BGM-109 Tomahawk

A ranar juma'a ne dai aka wayi gari da labarin yadda Amurka ta kai harin makami mai linzami da...

Bincike: Bidiyon Ali Baba Fagge da ke yawo a TikTok na zagin matar Ganduje haɗin AI ne

Iƙirari: A makon da ya gabata, wani bidiyo ya fara yawo sosai a kafar sada zumunta ta TikTok, wanda...

Karanta wannan

Labarin cewa Aisha Buhari ta amince ta auri Sheikh Isa Ali Pantami ƙarya ne

Tun bayan kammala iddar tsohuwar matar shugaban kasa Muhammadu...

Gwamna Abba Kabir Yusuf bai cire Mustapha Kwankwaso daga muƙaminsa ba

A ƙarshen watan Disemba ne dadi aka sami labarin...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar