BindiddigiIna gaskiyar cewa an kirkiri sabbin jihohi?

Ina gaskiyar cewa an kirkiri sabbin jihohi?

-

Hukunci: Ƙarya ne
Majalisar dattawa ta bakin mai magana da yawunta ta musanta cewa majalisar ta amince da kirkirar sabbin jihohi. Sannan babu wata sahihiyar gidan jarida data rawaito ko wallafa labarin. Wannan yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa labarin an kirkiri sabbin jihohi 31 karya ne.
Shekara da shekaru dai wasu na neman a kirkiri wasu sabbin jihohi a Najeriya.
Tun bayan lokacin mulkin Soji dai ba’a kara kirkirar koda sabuwar jiha guda daya ba.
Ikirari:
Akwai dai labarin dake yaduwa matuka a shafukan sada zumunta daban-daban dake ikirarin cewa majalisun tarayya sun amince da kirkirar sabbin jihohi.
Wani shafin Facebook mai suna Abba Sani Pantami ya wallafa wannan labari inda ya sami tofa albarkacin baki wato comment sama da dubu daya da dari uku. ((https://www.facebook.com/share/p/16tDVCE6c5/?))
Labarin karya kan kirkirar sabbin jihohi
Haka zalika wani shafin na Facebook mai suna Nigeria Arewa shima ya wallafa wannan labari. ((https://www.facebook.com/share/p/1BzytoxNGF/?))
Wani shafin TiKTok mai suna Jabir Kaura shima yayi ikirarin amincewa da sabbin jihohi. ((https://vm.tiktok.com/ZMSnyUSxV/))
Bincike:
Binciken kafar tantance labarai ta Alkalanci ya gano cewa akwai bukatar neman kirkirar jihohi 31 dake gaban majalisun tarraya biyu.
A watan Fabrairu ne dai kwamitin yiwa kundin tsarin mulki kwaskwarima na majalisar wakilan ya gabatar da bukatar kirkirar jihohi 31.
Mataimakin kakakin majalisar wakilai Benjamin Kalu ya bayyana bukatar kirkirar sabbin jihohin, yayin wani zaman majalisar.
Sunayen sabbin jihohin da ake son kirkira;
Okun, Okura, da Confluence daga Kogi;
Benue Ala da Apa daga Benue;
FCT State;
Amana daga Adamawa;
Katagum daga Bauchi;
Savannah daga Borno;
Muri daga Taraba;
New Kaduna da Gurara daga  Kaduna;
Tiga da Ari daga Kano;
Kainji daga Kebbi;
Etiti, Orashi, Adada, Orlu, da Aba daga kudu maso gabas.
Sauran sune Ogoja daga Cross River; Warri, Ori, and Obolo daga kudu maso kudu;
Sannan akwai  Torumbe, Ibadan, Lagoon, Ijebu, da Oke Ogun/Ijesha daga kudu maso yamma.
Bayan gabatar da wannan bukata dai majalisun tarayyar biyu dole suyi zama daban-daban, da kuma jin bakin masu ruwa da tsaki kafin majalisun su amince da wannan bukata.
Mai magana da yawun majalisar dattawan Najeriya ya musanta labarin dake yaduwa cewa sun amince da kirkirar sabbin jihohi.
Babu wata sahihiyar gidan jarida daya buga ko wallafa wannan labari.
Sakamakon bincike:
Bisa musanta amincewa da kirkirar sabbin jihohi da mai magana da yawun majalisar dattawa yayi da kuma kasa samun wannan labari a kowacce sahihiyar kafar yada labarai duk da girmansa. Kafar tantance labarai ta Alkalanci bata sami wani waje da aka rawaito cewa anyi zaman amince da wannan batu ba balle batun zaman masu ruwa da tsaki. Wadannan dalilai na rashin ingantattun bayanai yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa labarin dake yaduwa kan an kirkiri sabbin jihohi karya ne.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Labarin cewa Aisha Buhari ta amince ta auri Sheikh Isa Ali Pantami ƙarya ne

Tun bayan kammala iddar tsohuwar matar shugaban kasa Muhammadu Buhari ake ta yada wasu labarai da iƙirarai kala-kala wanda...

Gwamna Abba Kabir Yusuf bai cire Mustapha Kwankwaso daga muƙaminsa ba

A ƙarshen watan Disemba ne dadi aka sami labarin cewa gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf zai sauya sheƙa...

Me yasa Amurka ta kai hari Sokoto?

Kasar Amurka ta takaddamar da hare-hare a wasu yankuna a arewacin Najeriya. Yanku nan sun hada da Arewa maso...

Duk da Iƙirarin gwamnatin Katsina Ameena Dikko Radda na da shafin Instagram tun 2018

Akwai wani hoto daya yaɗu matuƙa game da yar gwamnan jahar Katsina mai suna Amina dikko Radda inda aka...

Abunda ya kamata ku sani dangane da makamin BGM-109 Tomahawk

A ranar juma'a ne dai aka wayi gari da labarin yadda Amurka ta kai harin makami mai linzami da...

Bincike: Bidiyon Ali Baba Fagge da ke yawo a TikTok na zagin matar Ganduje haɗin AI ne

Iƙirari: A makon da ya gabata, wani bidiyo ya fara yawo sosai a kafar sada zumunta ta TikTok, wanda...

Karanta wannan

Labarin cewa Aisha Buhari ta amince ta auri Sheikh Isa Ali Pantami ƙarya ne

Tun bayan kammala iddar tsohuwar matar shugaban kasa Muhammadu...

Gwamna Abba Kabir Yusuf bai cire Mustapha Kwankwaso daga muƙaminsa ba

A ƙarshen watan Disemba ne dadi aka sami labarin...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar