BindiddigiTattalin ArzikiIkirarin Tinubu na shigowar kudaden zuba jari dag kasashen...

Ikirarin Tinubu na shigowar kudaden zuba jari dag kasashen waje daya kai dala biliyan talatin $30bn ba dai-dai bane

-

Shugaba Bola Tinubu a cikin jawabinsa na ranar daya ga watan Oktoba wato ranar bikin yan cin kan kasar yayi ikirarin cewa cikin shekara guda na mulkinsa kasar ta sami shigowar masu zuba jari daga kasashen waje daya kai sama da dala biliyan talatin $30bn.

Hukumar kididdiga ta kasar wato NBS takan fitar da yawan kudaden da suka shigo Najeriya duk watanni uku wato kwata wanda ya hada da saka hannun jari daga kasashen waje.

A farkon watanni uku na wannan shekara ta 2024, Najeriya ta sami shigowar kudade daga masu sanya hannun jari da suka kai dala miliyan $119.18m a yayin da a tsakanin Afrilu zuwa Satumba kuma kasar ta sami shigowar dala miliyan $183.97. Haka zalika a watanni ukun karshen shekarar 2023 kuwa kasar ta sami shigowar dala miliyan $59.77m a inda watanni Yuli, Agusta da satumbar 2023 kuwa kasar ta sami shigowar kudaden zuba jari dala $86.03 wato watannin da Tinubu ya karbi mulki kenan.

Idan aka lissafa kididdiga daga hukumar ta NBS za’a iya cewa daga watan Afrilun 2023 zuwa watan Maris din 2024 kudin zuba jari daga kasashen waje zai tashi dala miliyan $448.95m wanda bai kai ko rabin biliyan dala daya ba.

Haka zalika babu wata shaida Ko alkaluma dake nuna cewa kasar ta sami shigowar kudaden zuba jari da suka kai dala biliyan $30bn a tsakanin watanni shida zuwa watanni tara na wannan shekarar ta 2024.

Sannan a cikin jawabin Tinubu yayi ikirarin cewa ya gaji dala biliyan $33bn a asusun ajiyar kasar wato foreign reserve. To sai dai alkaluma daga baban bankin kasar ya nuna cewa abinda ya gada daga Muhammadu Buhari yafi haka domin kuwa an bar masa dala biliyan $35bn maimakon $33billion da yayi ikirari.

Iƙirarin na shugaba Tinubu dai ba gaskiya bane. Wato a turance ake cewa misleading Ko incorrect.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Shin Nijar ta rabu da Faransanci?

Tun bayan labarin amincewa da kuma ayyana Hausa a matsayin harshen kasa mutane ke ta wallafa labarin cewa Nijar...

Labaran ƙarya ne ke haddasa ƙiyayya tsakanin ‘yan kudu da ‘yan arewa

Shekara da shekaru dai ana samun rasa rayuka da dukiyoyin al’ummar arewacin Najeriya a kudancin kasar. Abubuwan da suka...

Labaran karya daga Burkina Faso na cigaba da yaduwa a Najeriya

  Da dama daga ‘yan Najeriya masu amfani da kafafen sada zumunta na cin karo da labarai kala-kala dangane da...

Najeriya-Saudiyya sun karyata labarin cewa za’a hana ‘yan kasar bizar shiga Saudiyya

Ma’aikatar harkokin wajen Najeriya ta karyata ikirarin karya da ke yawo a kafafen sadarwa na zamani, wanda ke cewa...

Ina gaskiyar cewa Amurka, Faransa ke neman haddasa faɗa tsakanin Sudan da Chadi?

  Duk lokacin da aka sami wata hatsaniya ko rikici tsakanin kasashe, wasu na amfani da wannan dama wajen yada...

Bidiyon ƴan sanda sunyi kame a Edo ƙarya ne, bidiyon ya faru a Ghana ne

  A yayin da ƴan Najeriya ke cigaba da Allah wadai da kisan wasu matafiya a jihar Edo, wasu na...

Karanta wannan

Shin Nijar ta rabu da Faransanci?

Tun bayan labarin amincewa da kuma ayyana Hausa a...

Labaran ƙarya ne ke haddasa ƙiyayya tsakanin ‘yan kudu da ‘yan arewa

Shekara da shekaru dai ana samun rasa rayuka da...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar