BindiddigiTattalin ArzikiIkirarin Tinubu na shigowar kudaden zuba jari dag kasashen...

Ikirarin Tinubu na shigowar kudaden zuba jari dag kasashen waje daya kai dala biliyan talatin $30bn ba dai-dai bane

-

Shugaba Bola Tinubu a cikin jawabinsa na ranar daya ga watan Oktoba wato ranar bikin yan cin kan kasar yayi ikirarin cewa cikin shekara guda na mulkinsa kasar ta sami shigowar masu zuba jari daga kasashen waje daya kai sama da dala biliyan talatin $30bn.

Hukumar kididdiga ta kasar wato NBS takan fitar da yawan kudaden da suka shigo Najeriya duk watanni uku wato kwata wanda ya hada da saka hannun jari daga kasashen waje.

A farkon watanni uku na wannan shekara ta 2024, Najeriya ta sami shigowar kudade daga masu sanya hannun jari da suka kai dala miliyan $119.18m a yayin da a tsakanin Afrilu zuwa Satumba kuma kasar ta sami shigowar dala miliyan $183.97. Haka zalika a watanni ukun karshen shekarar 2023 kuwa kasar ta sami shigowar dala miliyan $59.77m a inda watanni Yuli, Agusta da satumbar 2023 kuwa kasar ta sami shigowar kudaden zuba jari dala $86.03 wato watannin da Tinubu ya karbi mulki kenan.

Idan aka lissafa kididdiga daga hukumar ta NBS za’a iya cewa daga watan Afrilun 2023 zuwa watan Maris din 2024 kudin zuba jari daga kasashen waje zai tashi dala miliyan $448.95m wanda bai kai ko rabin biliyan dala daya ba.

Haka zalika babu wata shaida Ko alkaluma dake nuna cewa kasar ta sami shigowar kudaden zuba jari da suka kai dala biliyan $30bn a tsakanin watanni shida zuwa watanni tara na wannan shekarar ta 2024.

Sannan a cikin jawabin Tinubu yayi ikirarin cewa ya gaji dala biliyan $33bn a asusun ajiyar kasar wato foreign reserve. To sai dai alkaluma daga baban bankin kasar ya nuna cewa abinda ya gada daga Muhammadu Buhari yafi haka domin kuwa an bar masa dala biliyan $35bn maimakon $33billion da yayi ikirari.

Iƙirarin na shugaba Tinubu dai ba gaskiya bane. Wato a turance ake cewa misleading Ko incorrect.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Ina gaskiyar Iƙirarin mai da waɗanda ake zargi da kisa a Kano zuwa kudancin Najeriya?

IƙirariWani bidiyo yana ta yaɗuwa a kafar sada zumunta ta TikTok wanda ke nuna cewa jami'an tsaro sun kwashe...

Ina gaskiyar labari da hotunan baiwa ƴan wasan Super Eagles gidaje da motoci

Bayan da aka kammala gasar cin kofin Nahiyar Afirka AFCON wanda Najeriya ta zo ta biyu, akwai labarai kala-kala...

Bidiyon da ake yaɗawa ba na waɗanda sukai kisan Ɗorayi bane 

Ƴan Najeriya dai na cigaba da jimami tare da Allah wadai da kisan wasu ƴan gida ɗaya su bakwai...

Hotunan samuwar makaman kariya zuwa Burkina Faso daga Rasha da China hadin AI ne

  Yayin da Rasha da ƙasar Sin ke ci gaba da tura makamai zuwa yankin Sahel, wani hoto da bidiyo...

Labarin cewa Aisha Buhari ta amince ta auri Sheikh Isa Ali Pantami ƙarya ne

Tun bayan kammala iddar tsohuwar matar shugaban kasa Muhammadu Buhari ake ta yada wasu labarai da iƙirarai kala-kala wanda...

Gwamna Abba Kabir Yusuf bai cire Mustapha Kwankwaso daga muƙaminsa ba

A ƙarshen watan Disemba ne dadi aka sami labarin cewa gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf zai sauya sheƙa...

Karanta wannan

Ina gaskiyar Iƙirarin mai da waɗanda ake zargi da kisa a Kano zuwa kudancin Najeriya?

IƙirariWani bidiyo yana ta yaɗuwa a kafar sada zumunta...

Ina gaskiyar labari da hotunan baiwa ƴan wasan Super Eagles gidaje da motoci

Bayan da aka kammala gasar cin kofin Nahiyar Afirka...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar