BindiddigiDuk da Iƙirarin gwamnatin Katsina Ameena Dikko Radda na...

Duk da Iƙirarin gwamnatin Katsina Ameena Dikko Radda na da shafin Instagram tun 2018

-

Hukunci: Ƙarya ne
Bisa samun cewa akwai shafi ko asusun Instagram da Ameena Dikko Radda ta buɗe tun 2018, kuma tayi verifying dinsa a 2025, tare da samun cewa mahaifiyarta Zulaihat Abdullahi Dikko na binta suka tabbatar da cewa Ameena Dikko Radda na da shafin Instagram, wannan yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa iƙirarin gwamnatin Katsina na cewa bata da wani shafin sada zumunta kwata-kwata ƙarya ne.

Akwai wani hoto daya yaɗu matuƙa game da yar gwamnan jahar Katsina mai suna Amina dikko Radda inda aka nuna  tare da wallafa wasu hotuna dake cewa tana neman kujerar Sanata a jahar Katsina kamar yanda kuke gani a wanna hoton.

Waɗannan hotuna dai sun yaɗu matuƙa a kafafen sada zumunta musamman Facebook.

Iƙirari:
Wani shafin Facebook ya wallafa hoton ‘yar gwamnan dake nuna cewa zata nemi kujerar Sanata a Jihar Katsina a cikin wani zaure wato group.
Gwamnatin Jihar Katsina ta fitar da sanarwa a hukumance, inda ta karyata wannan zargi baki daya, tare da bayyana cewa shafin da ake yadawa na bogi ne.
Sanarwar gwamnatin yayi iƙirarin cewa ƴar Gwamna Radda ba ta neman kowacce kujera ta zabe ,har Ila yau sun kara da Sanar da cewa , ba ta da shafin Facebook ko ma  wani shafin sada zumunta  kwata-kwata.
Wasu manyan gidajen jaridu na Hausa sun rawaito wannan labari misali Arewa Update  da kuma DCL.
Yayin da gwamnatin ta ƙaryata wancan labari sai kuma mutane suke tambayar anya gaskiya ne Ameena Dikko Radda bata da wani shafin kafar sada zumunta?
Wannan yasa Alkalanci zurfafa bincike wajen gano gaskiyar labarin cewa shin Ameena Dikko Radda bata da shafi a kafafen sada zumunta kamar yadda gwamnatin jahar Katsina ta bayyana?
TikTok:
Da farko dai Alkalanci ta fara da Duba kafar TikTok inda tasamu shafuka sama da 50 da suke amfani da sunan Amina Dikko Radda ba tare da samun wani gamsasshe da za a iya cewa nata ne ba. Wato dai Alkalanci bata sami ɗaya da zata iya alaƙanta shi da Ameena Dikko Radda ba.
Facebook:
Haka zalika Alkalanci ta garzaya Facebook inda shima aka samu shafuka da dama da suke amfani da sunan ƴar gwamna Radda.
Akwai wani shafin main suna Amina Dikko Radda wanda hotunan ta ne har ƙaryata labarin yake wato yana nuna wannan shafin shine sahihi mallakar Ameena Dikko Radda to amma Alkalanci bata sami wani tabbacin shafin mallakar Ameena bane duk da cewa akwai mutane sama da dubu goma sha huɗu dake bibiyar shafin. Mutane da dama a comment section sun aminta da cewa shafin sahihi ne.
Instagram:
Sai kuma Alkalanci ta garzaya zuwa Instagram inda kamar sauran shafukan akwai da dama dake ɗauke da sunan Ameena Dikko Radda to amma a Instagram akwai wanda ya tabbata na ƴar gidan gwamnan Katsina ce Ameena Dikko Radda ne.
Ta buɗe wannan shafin na Instagram a watan Agustan 2018 kuma tayi verifying ɗinsa a shekarar 2025.
Sahihin Shafin Ameena Dikko Radda na Instagram
Haka zalika da muka duba shafin Instagram na matar gwamna Radda mai suna Zulaihat Abdullahi Dikko wacce ita ce mahaifiyar Ameena Alkalanci ta ga cewa tana bin shafin Ameena Dikko Radda.
Shaidar dake nuna matar gwamna Radda na bin Ameena Dikko Radda a Instagram
Sannan mutane da dama sun tabbatar da cewa tana gudanar da Instagram live lokaci zuwa lokaci.
Sakamakon bincike:
Bisa samun waɗannan hujjoji da suka tabbatar da cewa Ameena Dikko Radda na da shafin Instagram yasa Alkalanci yanke hukuncin cewa iƙirarin gwamnatin Katsina na cewa bata da wani shafin sada zumunta kwata-kwata ƙarya ne.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sababbin Labarai

Bidiyon da ake yaɗawa ba na waɗanda sukai kisan Ɗorayi bane 

Ƴan Najeriya dai na cigaba da jimami tare da Allah wadai da kisan wasu ƴan gida ɗaya su bakwai...

Hotunan samuwar makaman kariya zuwa Burkina Faso daga Rasha da China hadin AI ne

  Yayin da Rasha da ƙasar Sin ke ci gaba da tura makamai zuwa yankin Sahel, wani hoto da bidiyo...

Labarin cewa Aisha Buhari ta amince ta auri Sheikh Isa Ali Pantami ƙarya ne

Tun bayan kammala iddar tsohuwar matar shugaban kasa Muhammadu Buhari ake ta yada wasu labarai da iƙirarai kala-kala wanda...

Gwamna Abba Kabir Yusuf bai cire Mustapha Kwankwaso daga muƙaminsa ba

A ƙarshen watan Disemba ne dadi aka sami labarin cewa gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf zai sauya sheƙa...

Me yasa Amurka ta kai hari Sokoto?

Kasar Amurka ta takaddamar da hare-hare a wasu yankuna a arewacin Najeriya. Yanku nan sun hada da Arewa maso...

Abunda ya kamata ku sani dangane da makamin BGM-109 Tomahawk

A ranar juma'a ne dai aka wayi gari da labarin yadda Amurka ta kai harin makami mai linzami da...

Karanta wannan

Bidiyon da ake yaɗawa ba na waɗanda sukai kisan Ɗorayi bane 

Ƴan Najeriya dai na cigaba da jimami tare da...

Hotunan samuwar makaman kariya zuwa Burkina Faso daga Rasha da China hadin AI ne

  Yayin da Rasha da ƙasar Sin ke ci gaba...

Kuna iya kuma soDANGANTAKA
An ba ku shawarar